< 2 Mosebok 7 >

1 Da sa Herren til Moses: Se, jeg har satt dig til en Gud for Farao, og Aron, din bror, skal være din profet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 Du skal tale alt det jeg byder dig; men Aron, din bror, skal tale til Farao, og han skal la Israels barn fare ut av sitt land.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 Men jeg vil forherde Faraos hjerte, og jeg vil gjøre mange tegn og under i Egyptens land.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 Farao skal ikke høre på eder; men jeg vil legge min hånd på Egypten og føre mine hærer, mitt folk, Israels barn, ut av Egyptens land ved store straffedommer.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 Og egypterne skal kjenne at jeg er Herren, når jeg rekker ut min hånd over Egypten og fører Israels barn ut fra dem.
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 Og Moses og Aron gjorde dette; som Herren hadde pålagt dem, således gjorde de.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Moses var åtti år gammel, og Aron tre og åtti år, da de talte til Farao.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 Og Herren sa til Moses og Aron:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 Når Farao taler til eder og sier: La mig få se et under av eder, da skal du si til Aron: Ta din stav og kast den ned foran Farao! Og den skal bli til en slange.
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 Så gikk Moses og Aron inn til Farao og gjorde som Herren hadde sagt; Aron kastet sin stav ned foran Farao og hans tjenere, og den blev til en slange.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Da lot Farao sine vismenn og trollmenn kalle, og de, Egyptens tegnsutleggere, gjorde det samme med sine hemmelige kunster;
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 de kastet hver sin stav, og de blev til slanger; men Arons stav slukte deres staver.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 Men Faraos hjerte blev forherdet, og han hørte ikke på dem, således som Herren hadde sagt.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 Da sa Herren til Moses: Faraos hjerte er hårdt; han vil ikke la folket fare.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Gå til Farao imorgen tidlig når han går ned til elven, og still dig i hans vei på elvebredden, og staven som blev skapt om til en slange, skal du ta i hånden.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 Og du skal si til ham: Herren, hebreernes Gud, har sendt mig til dig og sier: La mitt folk fare, så de kan tjene mig i ørkenen! Men du har like til nu ikke villet lyde.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Sa sier Herren: På dette skal du kjenne at jeg er Herren: Se, nu slår jeg med denne stav som jeg har i min hånd, på vannet i elven, og det skal bli til blod,
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 og fiskene i elven skal dø, og elven skal lukte ille, så egypterne skal vemmes ved å drikke vannet.
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 Og Herren sa til Moses: Si til Aron: Ta din stav og rekk ut din hånd over egypternes vann, over deres elver, over deres kanaler og over deres sjøer og over alle deres dammer, og de skal bli til blod, og det skal være blod i hele Egyptens land, både i trekar og i stenkar.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 Og Moses og Aron gjorde som Herren hadde sagt; han løftet staven og slo på vannet i elven så de så på det, både Farao og hans tjenere; da blev alt vannet i elven til blod,
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 og fiskene i elven døde, og elven luktet ille, så egypterne ikke kunde drikke vannet, og det var blod i hele Egyptens land.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 Men Egyptens tegnsutleggere gjorde det samme med sine hemmelige kunster, og Faraos hjerte blev forherdet, og han hørte ikke på dem, således som Herren hadde sagt.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 Og Farao vendte sig om og gikk hjem til sitt hus og la heller ikke dette på hjerte.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 Men alle egypterne gravde rundt omkring elven efter drikkevann; for de kunde ikke drikke elvevannet.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 Så gikk det syv dager efterat Herren hadde slått elven.
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.

< 2 Mosebok 7 >