< 2 Mosebok 33 >

1 Og Herren talte til Moses: Dra nu bort herfra, både du og det folk som du har ført op fra Egyptens land, til det land jeg tilsvor Abraham, Isak og Jakob, da jeg sa: Din ætt vil jeg gi det;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
2 og jeg vil sende en engel foran dig og drive ut kana'anittene, amorittene og hetittene og ferisittene og hevittene og jebusittene.
Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
3 Dra op til et land som flyter med melk og honning; jeg vil ikke selv dra op med dig, fordi du er et hårdnakket folk; jeg vilde ellers komme til å ødelegge dig på veien.
Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
4 Da folket hørte denne hårde tale, sørget de, og ingen tok sine smykker på sig.
Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
5 For Herren sa til Moses: Si til Israels barn: I er et hårdnakket folk; drog jeg endog bare et øieblikk op med dig, så måtte jeg ødelegge dig; men legg nu dine smykker av dig, så jeg kan vite hvad jeg skal gjøre med dig.
Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
6 Da tok Israels barn sine smykker av og bar dem ikke mere, efterat de hadde draget fra fjellet Horeb.
Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
7 Men Moses tok et telt og slo det op utenfor leiren et godt stykke fra; han kalte det sammenkomstens telt, og enhver som søkte Herren, gikk ut til sammenkomstens telt utenfor leiren.
Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
8 Og hver gang Moses gikk ut til teltet, reiste hele folket sig, og de stod hver i døren til sitt telt og så efter Moses, til han var kommet inn i teltet.
A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
9 Og når Moses var kommet inn i teltet, da senket skystøtten sig og stod i døren til teltet, og han talte med Moses.
Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
10 Og alt folket så skystøtten stå i døren til teltet, og alt folket reiste sig og bøide sig hver i døren til sitt telt.
Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
11 Og Herren talte til Moses åsyn til åsyn, likesom en mann taler med sin næste. Så vendte han tilbake til leiren, men hans tjener Josva, Nuns sønn, en ung mann, vek ikke fra teltet.
Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
12 Og Moses sa til Herren: Se, du sier til mig: Før dette folk op! Men du har ikke latt mig vite hvem du vil sende med mig, enda du selv har sagt: Jeg kjenner dig ved navn, og du har funnet nåde for mine øine.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
13 Dersom jeg nu har funnet nåde for dine øine, så la mig se din vei, så jeg kan kjenne dig og finne nåde for dine øine, og kom i hu at dette folk er ditt folk!
In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
14 Da sa han: Mitt åsyn skal gå med, og jeg vil føre dig til hvile.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
15 Men han sa til ham: Dersom ditt åsyn ikke går med, da la oss ikke dra op herfra!
Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
16 Hvorav kan jeg da vite at jeg har funnet nåde for dine øine, jeg og ditt folk, medmindre du går med oss, så jeg og ditt folk blir æret fremfor alle folkeslag på jorden?
Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
17 Da sa Herren til Moses: Også det du nu ber om, vil jeg gjøre; for du har funnet nåde for mine øine, og jeg kjenner dig ved navn.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
18 Men han sa: La mig da få se din herlighet!
Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
19 Og han sa: Jeg vil la all min godhet gå forbi ditt åsyn, og jeg vil rope ut Herrens navn for ditt åsyn; for jeg vil være nådig mot den som jeg er nådig imot, og miskunne mig over den som jeg miskunner mig over.
Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
20 Og han sa: Du kan ikke se mitt åsyn; for intet menneske kan se mig og leve.
Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
21 Derefter sa Herren: Se, her tett ved mig er et sted; still dig der på berget,
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
22 og når min herlighet går forbi, da vil jeg la dig stå i fjellkløften, og jeg vil dekke med min hånd over dig til jeg er gått forbi;
A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
23 så vil jeg ta min hånd bort; da kan du se mig bakfra, men mitt åsyn kan ingen se.
Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”

< 2 Mosebok 33 >