< 2 Mosebok 19 >

1 På tremåneders-dagen efterat Israels barn var gått ut av Egyptens land, kom de til Sinai ørken.
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 De brøt op fra Refidim og kom til Sinai ørken og slo leir i ørkenen, og Israel leiret sig der midt imot fjellet. -
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 Men Moses steg op til Gud, og Herren ropte til ham fra fjellet og sa: Så skal du si til Jakobs hus og kunngjøre for Israels barn:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 I har sett hvad jeg har gjort med egypterne, og hvorledes jeg har båret eder på ørnevinger og ført eder til mig.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 Dersom I nu lyder min røst og holder min pakt, da skal I være min eiendom fremfor alle folk; for hele jorden hører mig til.
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 Og I skal være mig et kongerike av prester og et hellig folk. Dette er de ord du skal tale til Israels barn.
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 Da Moses kom tilbake, kalte han folkets eldste til sig og bar frem for dem alle disse ord som Herren hadde pålagt ham.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 Da svarte folket alle som én og sa: Alt det Herren har sagt, vil vi gjøre. Og Moses bar folkets ord tilbake til Herren.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 Da sa Herren til Moses: Se, jeg vil komme til dig i en tykk sky, så folket kan høre når jeg taler med dig, og alltid tro på dig. Og Moses bar folkets ord frem for Herren.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 Og Herren sa til Moses: Gå til folket og la dem hellige sig idag og imorgen og tvette sine klær,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 og la dem holde sig rede den tredje dag; for på den tredje dag skal Herren stige ned på Sinai berg for hele folkets øine.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 Og du skal avmerke en grense for folket rundt omkring og si: Vokt eder for å stige op på fjellet eller røre ved dets fot! Enhver som rører ved fjellet, skal visselig late livet;
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 ingen hånd skal røre ved ham, han skal stenes eller skytes; enten det er dyr eller mennesker, skal de ikke leve. Når basunen lyder med lange toner, da skal de stige op på fjellet.
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 Så gikk Moses ned fra fjellet til folket, og han lot folket hellige sig og tvette sine klær.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 Og han sa til folket: Hold eder rede den tredje dag, kom ikke nær nogen kvinne!
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 Så skjedde det den tredje dag da morgenen brøt frem, da tok det til å tordne og lyne, og det la sig en tung sky over fjellet, og det hørtes en sterk basunlyd; da skalv alt folket som var i leiren.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 Men Moses førte folket ut av leiren til møte med Gud, og de stilte sig nedenfor fjellet.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 Og hele Sinai berg stod i røk, fordi Herren var steget ned på det i ild, og røken av det steg op som røken av en ovn, og hele fjellet skalv.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 Og basunens lyd tok til og blev sterkere og sterkere; Moses talte, og Gud svarte ham med lydelig røst.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 Og Herren steg ned på Sinai berg, på fjellets topp; og Herren kalte Moses op på fjellets topp, og Moses steg op.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 Og Herren sa til Moses: Stig ned og advar folket, så de ikke trenger sig frem til Herren for å se ham, for da kommer mange av dem til å falle.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 Også prestene, de som treder Herren nær, skal hellige sig, forat Herren ikke skal bryte inn blandt dem.
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 Da sa Moses til Herren: Folket kan ikke stige op på Sinai berg; for du har selv advart oss og sagt at vi skulde avmerke en grense om fjellet og hellige det.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 Og Herren sa til ham: Stig nu ned og kom så her op igjen, både du og Aron; men prestene og folket må ikke trenge sig frem og stige op til Herren, forat han ikke skal bryte inn blandt dem.
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 Da steg Moses ned til folket og sa det til dem.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.

< 2 Mosebok 19 >