< 2 Tessalonikerne 3 >

1 For øvrig, brødre, bed for oss at Herrens ord må ha fremgang og bli forherliget likesom hos eder,
A ƙarshe,’yan’uwa, ku yi mana addu’a domin saƙon Ubangiji yă yi saurin bazuwa a kuma girmama shi, kamar yadda yake a wurinku.
2 og at vi må bli fridd fra de vrange og onde mennesker; for troen er ikke alles sak.
Ku kuma yi addu’a yadda za a cece mu daga mugayen mutane masu mugunta, gama ba kowa ba ne yake da bangaskiya.
3 Men Herren er trofast; han skal styrke eder og bevare eder fra det onde.
Ubangiji mai aminci ne, zai ƙarfafa ku, yă kuma tsare ku daga mugun nan.
4 Vi har den tillit til eder i Herren at I både gjør og herefter vil gjøre det vi byder eder.
Muna da tabbaci cikin Ubangiji cewa kuna bin umarnai da muka yi muku, za ku kuma ci gaba da yin abubuwan da muka umarta.
5 Og Herren styre eders hjerter til å elske Gud og til å vente på Kristus med tålmodighet!
Bari Ubangiji yă bi da zukatanku ga ƙaunan nan ta Allah da kuma jimirin nan na Kiristi.
6 Men vi byder eder, brødre, i vår Herre Jesu Kristi navn at I skal dra eder tilbake fra enhver bror som vandrer utilbørlig og ikke efter den lærdom som de fikk av oss.
A cikin sunan Ubangiji Yesu Kiristi, muna muku umarni,’yan’uwa, da ku kiyaye kanku daga kowane ɗan’uwa mai zaman banza da ba ya rayuwa bisa ga koyarwar da kuka karɓa daga wurinmu.
7 I vet jo selv hvorledes I bør efterfølge oss; for vi levde ikke utilbørlig iblandt eder,
Gama ku kanku kun san yadda ya kamata ku bi gurbinmu. Ba mu yi zaman banza sa’ad da muke tare da ku ba,
8 heller ikke åt vi brød hos nogen for intet, men med strev og møie arbeidet vi natt og dag, forat vi ikke skulde være nogen av eder til byrde;
ba mu kuwa ci abincin kowa ba tare da ba mu biya ba. A maimakon haka, mun yi aiki dare da rana, muna fama muna wahala kuma don kada mu nawaita wa waninku.
9 ikke fordi vi ikke har rett til det, men for å gi eder et forbillede i oss, forat I skulde efterfølge oss;
Mun yi wannan, ba don ba mu da’yancin karɓar irin taimakon nan ba ne, sai dai domin mu zama gurbin da za ku bi.
10 for da vi var hos eder, bød vi eder jo og dette at hvis nogen ikke vil arbeide, skal han heller ikke ete.
Ko ma a sa’ad da muke tare da ku, mun ba ku wannan umarni cewa, “In mutum ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci.”
11 For vi hører at nogen iblandt eder vandrer utilbørlig og ikke arbeider, men gir sig av med ting som ikke kommer dem ved.
Mun ji cewa waɗansunku suna zaman banza. Ba sa aikin kome; sai shisshigi kurum.
12 Men sådanne byder og formaner vi i den Herre Jesus Kristus at de skal arbeide i stillhet og ete sitt eget brød.
Irin waɗannan mutane muna ba da umarni muna kuma gargaɗe su cikin Ubangiji Yesu Kiristi su natsu su kuma nemi abincin da suke ci.
13 Men I, brødre, bli ikke trette av å gjøre det som rett er!
Game da ku kuma’yan’uwa, kada ku gaji da yin abin da yake daidai.
14 Men dersom nogen ikke lyder vårt ord her i brevet, da merk eder ham; ha ingen omgang med ham, forat han må gå i sig selv,
In wani bai yi biyayya da umarninmu a wannan wasiƙa ba, sai fa ku lura da shi. Kada ku haɗa kai da shi, don yă ji kunya.
15 og hold ham ikke for en fiende, men forman ham som en bror!
Duk da haka kada ku mai da shi abokin gāba, sai dai ku gargaɗe shi a matsayin ɗan’uwa.
16 Og han, fredens Herre, gi eder fred alltid, i alle måter! Herren være med eder alle!
Yanzu, bari Ubangiji mai salama kansa yă ba ku salama a kowane lokaci da kuma a ta kowace hanya. Ubangiji yă kasance tare da ku duka.
17 Hilsen med min, Paulus' hånd; dette er et merke i hvert brev; således skriver jeg:
Ni, Bulus, nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna, wannan ce shaida a kowace wasiƙata, haka nake rubutu.
18 Vår Herre Jesu Kristi nåde være med eder alle!
Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku duka.

< 2 Tessalonikerne 3 >