< 2 Tessalonikerne 1 >

1 Paulus og Silvanus og Timoteus - til tessalonikernes menighet i Gud vår Fader og den Herre Jesus Kristus:
Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
2 Nåde være med eder og fred fra Gud vår Fader og den Herre Jesus Kristus!
Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
3 Vi er skyldige til å takke Gud alltid for eder, brødre, som tilbørlig er, fordi eders tro vokser rikelig, og kjærligheten til hverandre tar til hos hver og en iblandt eder alle,
Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
4 så vi selv roser oss av eder i Guds menigheter for eders tålmodighet og tro under alle eders forfølgelser og de trengsler som I holder ut
Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
5 - et varsel om Guds rettferdige dom - forat I skal finnes verdige til Guds rike, det som I og lider for,
Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
6 så sant det er rettferdig for Gud å gi dem som trenger eder, trengsel til vederlag,
Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
7 men eder som trenges, ro sammen med oss, når vår Herre Jesus åpenbares fra himmelen med sin makts engler,
yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
8 med luende ild, når han tar hevn over dem som ikke kjenner Gud, og over dem som ikke er lydige mot vår Herre Jesu evangelium,
Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
9 de som skal lide straff, en evig fortapelse bort fra Herrens åsyn og fra hans makts herlighet, (aiōnios g166)
Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
10 når han kommer på hin dag for å vise sig herlig i sine hellige og underfull i alle de troende - for trodd blev vårt vidnesbyrd til eder.
a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
11 Derfor beder vi og alltid for eder at vår Gud må akte eder verdige for sitt kall og mektig fylle eder med all lyst til det gode og virksomhet i troen,
Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
12 forat vår Herre Jesu navn må bli herliggjort i eder, og I i ham, efter vår Guds og den Herre Jesu Kristi nåde.
Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.

< 2 Tessalonikerne 1 >