< 2 Samuel 9 >

1 David sa: Er det ennu nogen tilbake av Sauls hus, så jeg kan gjøre vel mot ham for Jonatans skyld?
Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
2 Nu var der i Sauls hus en tjener som hette Siba; han blev kalt til David, og kongen sa til ham: Er du Siba? Han svarte: Ja, din tjener heter så.
To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
3 Da sa kongen: Er det ikke ennu nogen tilbake av Sauls hus, så jeg kunde gjøre Guds miskunnhet mot ham? Siba svarte: Det er ennu en sønn av Jonatan, en som er lam i begge føtter.
Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
4 Kongen spurte: Hvor er han? Siba svarte: Han er i huset hos Makir, sønn av Ammiel, i Lo-Debar.
Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
5 Så sendte kong David bud og hentet ham fra Makirs, Ammiels sønns hus i Lo-Debar.
Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
6 Og da Mefiboset, sønn av Jonatan, Sauls sønn, kom inn til David, kastet han sig ned med ansiktet mot jorden. Og David sa: Mefiboset! Han svarte: Her er din tjener.
Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
7 David sa til ham: Vær ikke redd! Jeg vil gjøre vel mot dig for Jonatans, din fars skyld og gi dig tilbake all Sauls, din fars jordeiendom, og du skal alltid ete ved mitt bord.
Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
8 Da kastet han sig ned og sa: Hvad er din tjener, at du lar ditt øie falle på en død hund som mig?
Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
9 Så kalte kongen på Siba, Sauls tjener, og sa til ham: Alt som har hørt Saul og hele hans hus til, har jeg gitt din herres sønn.
Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
10 Og du skal dyrke jorden for ham, du og dine sønner og dine tjenere, og høste inn for ham, så din herres sønn kan ha brød å ete, men selv skal Mefiboset, din herres sønn, alltid ete ved mitt bord. Siba hadde femten sønner og tyve tjenere.
Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
11 Da sa Siba til kongen: Din tjener skal i alle måter gjøre således som min herre kongen befaler sin tjener. Men Mefiboset skal ete ved mitt bord som en av kongens sønner sa kongen.
Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
12 Mefiboset hadde en liten sønn som hette Mika, og alle som bodde i Sibas hus, var Mefibosets tjenere.
Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
13 Men selv bodde Mefiboset i Jerusalem; for han åt alltid ved kongens bord; og han var lam i begge sine føtter.
Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.

< 2 Samuel 9 >