< 2 Samuel 6 >

1 David samlet atter alt utvalgt mannskap i Israel - tretti tusen mann.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 Og David og alt folket som var hos ham, tok ut og drog fra Ba'ale-Juda for å føre Guds ark op derfra, den som kalles med Herrens navn - med Herrens, hærskarenes Guds navn, han som troner på kjerubene.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 De satte Guds ark på en ny vogn og førte den bort fra Abinadabs hus, som lå på haugen; og Ussa og Ahjo, Abinadabs sønner, kjørte den nye vogn.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 Således førte de Guds ark bort fra Abinadabs hus, som lå på haugen, og fulgte med den, og Ahjo gikk foran arken.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 Og David og hele Israels hus lekte for Herrens åsyn til alle slags strengelek av cypresstre, både citarer og harper og trommer og bjeller og cymbler.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Da de kom til Nakons treskeplass, rakte Ussa sin hånd ut og tok fatt i Guds ark; for oksene var blitt ustyrlige.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 Da optendtes Herrens vrede mot Ussa, og Gud slo ham der for hans forseelse, så han døde der ved Guds ark.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 Men David blev ille til mote, fordi Herren hadde slått Ussa ned; derfor er dette sted blitt kalt Peres-Ussa like til denne dag.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 Den dag blev David opfylt av frykt for Herren og sa: Hvorledes skulde Herrens ark kunne komme inn til mig?
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 Og David vilde ikke flytte Herrens ark op til sig i Davids stad, men lot den føre bort til gittitten Obed-Edoms hus.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 Herrens ark blev stående i gittitten Obed-Edoms hus i tre måneder, og Herren velsignet Obed-Edom og alt hans hus.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 Så kom det nogen og fortalte kong David at Herren hadde velsignet Obed-Edoms hus og alt det han hadde, for Guds arks skyld. Da tok David avsted og førte Guds ark fra Obed-Edoms hus op til Davids stad med stor glede.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 Og da de som bar Herrens ark, hadde gått seks skritt frem, ofret han okser og gjøkalver.
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 Og David danset av all makt for Herrens åsyn - han hadde en livkjortel av lerret på.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 Således førte David og hele Israels hus Herrens ark op med fryderop og basunklang.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 Da nu Herrens ark kom inn i Davids stad, så Mikal, Sauls datter, ut igjennem vinduet, og hun så kong David hoppe og danse for Herrens åsyn, og hun foraktet ham i sitt hjerte.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 Så førte de da Herrens ark inn og satte den på sitt sted midt i det telt som David hadde reist for den, og David ofret brennoffer for Herrens åsyn og takkoffer.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 Og da David var ferdig med å ofre brennofferet og takkofferne, velsignet han folket i Herrens, hærskarenes Guds navn.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 Og han utdelte til alt folket, til hver enkelt av hele Israels mengde, både mann og kvinne, et brød og et stykke kjøtt og en rosinkake. Så drog alt folket hjem, hver til sitt hus.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 Da David kom hjem igjen for å velsigne sitt hus, gikk Mikal, Sauls datter, ut imot ham og sa: Hvor høit Israels konge er blitt æret idag - han som idag har blottet sig for øinene på sine tjeneres piker, som løse folk pleier å gjøre!
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 Da sa David til Mikal: For Herrens åsyn, han som utvalgte mig fremfor din far og fremfor hele hans hus og satte mig til fyrste over Herrens folk, over Israel - for Herrens åsyn har jeg danset;
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 og jeg vil gjøre mig ennu ringere enn så og bli liten i mine egne øine, og de tjenestepiker du talte om, sammen med dem vil jeg æres.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Men Mikal, Sauls datter, blev barnløs til sin dødsdag.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >