< 2 Samuel 22 >

1 David kvad denne sang for Herren den dag da Herren hadde utfridd ham av alle hans fienders hånd og av Sauls hånd.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 Og han sa: Herren er min klippe og min festning og min redder,
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 min klippefaste Gud, som jeg setter min lit til, mitt skjold og min frelses horn, min borg og min tilflukt, min frelser; fra vold frelser du mig.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 Jeg påkaller den Høilovede, Herren, og blir frelst fra mine fiender.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Dødens bølger omspente mig, fordervelsens strømmer forferdet mig.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Dødsrikets rep omgav mig, dødens snarer overfalt mig. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
7 I min trengsel påkalte jeg Herren, og jeg ropte til min Gud; han hørte fra sitt tempel min røst, og mitt skrik kom for hans ører.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Da rystet og bevet jorden, himmelens grunnvoller skalv, og de rystet; for hans vrede var optendt.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Det steg røk op av hans nese, og fortærende ild fra hans munn; glør brente ut av ham.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 Og han bøide himmelen og steg ned, og det var mørke under hans føtter.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 Og han fór på kjeruber og fløi, og han lot sig se på vindens vinger.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 Og han gjorde mørke til skjul rundt omkring sig, vannmasser, tykke skyer.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 Frem av glansen foran ham brente gloende kull.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 Herren tordnet fra himmelen, den Høieste lot sin røst høre.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 Og han utsendte piler og spredte dem omkring - lyn og forvirret dem.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Da kom havets strømmer til syne; jordens grunnvoller blev avdekket ved Herrens trusel, for hans neses åndepust.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 Han rakte sin hånd ut fra det høie, han grep mig; han drog mig op av store vann.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Han fridde mig ut fra min sterke fiende, fra mine avindsmenn; for de var mig for mektige.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 De overfalt mig på min motgangs dag; men Herren blev min støtte.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 Og han førte mig ut i fritt rum; han frelste mig, for han hadde behag i mig.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 Herren gjengjeldte mig efter min rettferdighet, han betalte mig efter mine henders renhet.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 For jeg tok vare på Herrens veier og vek ikke i ondskap fra min Gud;
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 for alle hans lover hadde jeg for øie, og fra hans bud vek jeg ikke,
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 og jeg var ulastelig for ham og voktet mig vel for min synd.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Og Herren gjengjeldte mig efter min rettferdighet, efter min renhet for hans øine.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Mot den fromme viser du dig from, mot den rettvise stridsmann viser du dig rettvis,
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 mot den rene viser du dig ren, mot den forvendte viser du dig vrang.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 Elendige folk frelser du, men dine øine er mot de overmodige; dem fornedrer du.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For du er mitt lys, Herre, og Herren opklarer mitt mørke.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For ved dig stormer jeg løs på fiendeskarer, ved min Gud springer jeg over murer.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 Gud, hans vei er fullkommen; Herrens ord er rent, han er et skjold for alle dem som setter sin lit til ham.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 For hvem er Gud foruten Herren, og hvem er en klippe foruten vår Gud?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Gud, han er mitt sterke vern og leder den ulastelige på hans vei.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Han gir ham føtter likesom hindene og stiller mig på mine høider.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Han oplærer mine hender til krig, så mine armer spenner kobberbuen.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Og du gir mig din frelse til skjold, og din mildhet gjør mig stor.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Du gjør rummet vidt for mine skritt under mig, og mine ankler vakler ikke.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 Jeg vil forfølge mine fiender og ødelegge dem, og jeg vender ikke tilbake før jeg har gjort ende på dem.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 Jeg gjør ende på dem og knuser dem, så de ikke kan reise sig; de faller under mine føtter.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Og du omgjorder mig med kraft til krig, du bøier mine motstandere under mig.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 Og mine fiender lar du vende mig ryggen, mine avindsmenn utrydder jeg.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 De ser sig om, men der er ingen frelser - efter Herren, men han svarer dem ikke.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Og jeg knuser dem som jordens støv; jeg sønderknuser dem, tramper dem ned som søle på gatene.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Og du redder mig fra mitt folks kamper, du bevarer mig til å være hode for hedninger; folkeferd som jeg ikke kjenner, tjener mig.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Fremmede kryper for mig; bare de hører om mig, blir de mig lydige.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Fremmede visner bort og går bevende ut av sine borger.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 Herren lever, og priset er min klippe, og ophøiet er min frelses klippefaste Gud,
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 den Gud som gir mig hevn og legger folkeferd under mig,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 og som fører mig ut fra mine fiender; over mine motstandere ophøier du mig, fra voldsmannen redder du mig.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Derfor vil jeg prise dig, Herre, blandt hedningene og lovsynge ditt navn.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Han gjør frelsen stor for sin konge, og han gjør miskunnhet mot sin salvede, mot David og mot hans ætt til evig tid.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

< 2 Samuel 22 >