< 2 Samuel 10 >

1 Så hendte det at Ammons barns konge døde, og Hanun, hans sønn, blev konge i hans sted.
Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Da sa David: Jeg vil vise Hanun, Nahas' sønn, vennskap, likesom hans far viste mig vennskap. Og David sendte nogen av sine tjenere for å trøste ham i hans sorg over sin far. Så kom da Davids tjenere til Ammons barns land.
Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
3 Da sa Ammons barns høvdinger til Hanun, sin herre: Tror du det er for å ære din far at David har sendt folk som skal trøste dig? Mon det ikke heller er for å utforske byen og utspeide den og så ødelegge den at David har sendt sine tjenere til dig?
sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
4 Da tok Hanun Davids tjenere og raket av halvdelen av deres skjegg og skar av deres klær midt på like til setet og lot dem så fare.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
5 Da dette blev meldt David, sendte han folk som skulde møte mennene, for de var grovelig vanæret; og kongen lot si: Bli i Jeriko til eders skjegg er vokset ut igjen, og kom så tilbake!
Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
6 Da nu Ammons barn så at de hadde gjort sig forhatt hos David, sendte de bud og leide syrerne fra Bet-Rehob og syrerne fra Soba, tyve tusen mann fotfolk, og kongen i Ma'aka med tusen mann og tolv tusen mann fra Tob.
Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
7 Da David hørte dette, sendte han Joab avsted med hele hæren, de krigsvante menn.
Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
8 Og Ammons barn rykket ut og stilte sig i fylking foran byporten; men syrerne fra Soba og Rehob og mennene fra Tob og Ma'aka stod for sig selv på marken.
Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
9 Da Joab så at han hadde fienden mot sig både foran og bak, valgte han ut en del av alt det utvalgte mannskap i Israel og stilte dem op mot syrerne.
Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
10 Men resten av folket overgav han til sin bror Abisai og stilte dem op mot Ammons barn.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
11 Og han sa: Dersom syrerne blir mig for sterke, skal du komme mig til hjelp, og dersom Ammons barn blir dig for sterke, skal jeg komme og hjelpe dig.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
12 Vær modig, og la oss vise oss modige i striden for vårt folk og for vår Guds byer, så får Herren gjøre hvad som er godt i hans øine!
Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
13 Så rykket Joab frem med sine folk til strid mot syrerne, og de flyktet for ham.
Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
14 Og da Ammons barn så at syrerne flyktet, så flyktet også de for Abisai og drog sig inn i byen. Da vendte Joab tilbake fra striden mot Ammons barn og kom til Jerusalem.
Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
15 Da syrerne så at de var blitt slått av Israel, samlet de sig igjen.
Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
16 Og Hadadeser sendte bud at de syrere som bodde på hin side av elven, skulde rykke ut; de kom til Helam, og Sobak, høvdingen over Hadadesers hær, førte dem.
Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
17 Da dette blev meldt David, samlet han hele Israel og gikk over Jordan og kom til Helam; og syrerne stilte sig op mot David og stred mot ham.
Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
18 Men syrerne flyktet for Israel, og David drepte blandt syrerne mannskapet på syv hundre vogner og firti tusen hestfolk, og Sobak, deres hærfører, såret han, så han døde der.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
19 Og da alle kongene som stod under Hadadeser, så at de var blitt slått av Israel, gjorde de fred med Israel og blev deres tjenere; og syrerne vågde ikke å hjelpe Ammons barn mere.
Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.

< 2 Samuel 10 >