< 2 Korintierne 5 >

1 For vi vet at om vårt legemes jordiske hus nedbrytes, så har vi en bygning av Gud, et hus som ikke er gjort med hender, evig i himlene. (aiōnios g166)
Mun san cewa idan wannan gidan da muke zaune a ciki ya rushe, muna da wani ginin daga wurin Allah. Gida ne wanda ba hannuwan mutane suka gina ba, amma madawwamin gida ne a cikin sama. (aiōnios g166)
2 For også mens vi er her til huse, sukker vi, fordi vi lenges efter å overklædes med vår bolig fra himmelen,
Domin a cikin wannan jiki muna gurnani, muna jira a suturta mu da wurin zaman mu na samaniya.
3 så sant vi skal bli funnet iklædd, ikke nakne.
Muna jiran wannan ne domin ta wurin suturtar da mu ba za a same mu tsirara ba.
4 For vi som er i denne hytte, sukker under byrden, fordi vi ikke vil avklædes, men overklædes, forat det dødelige kan bli opslukt av livet.
Gama babu shakka yayinda muke cikin wannan alfarwa, muna gurnani, muna nawaita. Ba mu so muyi zaman hutanci. Maimakon haka, muna so a suturtar da mu, domin rai ya hadiye abu mai mutuwa.
5 Men den som har satt oss i stand just til dette, er Gud, han som og har gitt oss Ånden til pant.
Wanda kuwa yake shirya mu domin ainihin wannan abu Allah ne, wanda ya ba mu Ruhu a matsayin alkawarin abinda ke zuwa.
6 Derfor er vi alltid frimodige og vet at så lenge vi er hjemme i legemet, er vi borte fra Herren;
Domin wannan mu zama da gabagadi koyaushe. Mu lura da cewa yayinda muka shagala cikin jiki, muna nesa da Ubangiji.
7 for vi vandrer i tro, ikke i beskuelse;
Gama bisa ga bangaskiya muke tafiya, ba bisa ga ganin ido ba.
8 vi er altså frimodige, og vil heller være borte fra legemet og være hjemme hos Herren.
Don haka muna da gabagadi. Mun gwammace mu rabu da jiki domin mu zauna tare da Ubangiji.
9 Derfor setter vi og vår ære i, enten vi er hjemme eller borte, å tekkes ham.
Sai muka maishe shi burinmu, ko muna cikin jiki ko nesa, mu gamshe shi.
10 For vi skal alle åpenbares for Kristi domstol, forat enhver kan få igjen det som er skjedd ved legemet, efter det som han har gjort, enten godt eller ondt.
Domin tilas dukanmu mu hallara a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, saboda kowa ya karbi sakamakon abubuwan da yayi cikin jiki, ko masu kyau ne ko marasa kyau.
11 Da vi altså kjenner frykten for Herren, søker vi å vinne mennesker, men for Gud er vi åpenbare; jeg håper og å være åpenbar for eders samvittigheter.
Don haka, domin mun san tsoron Ubangiji, muna rinjayar mutane. Allah na ganin yadda muke a fili. Ina fatan hakan a fili take ga lamirinku.
12 Vi gir oss nu ikke atter skussmål for eder; men vi gir eder leilighet til å rose eder av oss, forat I kan ha noget å sette imot dem som roser sig av det de er i det utvortes og ikke i hjertet.
Ba muna kokarin mu rinjaye ku domin ku kalle mu a matsayin amintattun mutane ba. Maimakon haka, muna ba ku dalilin yin takama da mu, domin ku sami amsar da za ku bada ga wadanda ke fahariya da kasancewarsu amma ba game da abinda ke zuciya ba.
13 For om vi er fra oss selv, da er det for Gud, og om vi er ved sans og samling, da er det for eder.
Gama idan mun fita daga hankulanmu, saboda Allah ne. Kuma idan muna cikin hankalinmu, domin ku ne.
14 For Kristi kjærlighet tvinger oss,
Domin kaunar Almasihu ta tilas ta mu, domin mun tabbatar da wannan: cewa mutum daya ya mutu domin kowa, kuma domin wannan duka sun mutu.
15 idet vi har opgjort dette med oss selv at én er død for alle, derfor er de alle død; og han døde for alle, forat de som lever, ikke lenger skal leve for sig selv, men for ham som er død og opstanden for dem.
Kuma Almasihu ya mutu domin kowa, domin wadanda ke raye kada su sake rayuwa domin kansu. A maimakon haka, su yi rayuwa domin shi wanda ya mutu kuma aka tashe shi.
16 Derfor kjenner vi fra nu av ikke nogen efter kjødet; har vi og kjent Kristus efter kjødet, så kjenner vi ham dog nu ikke lenger således.
Domin wannan dalili, daga yanzu ba za mu kara shar'anta kowa bisa ga ma'aunin 'yan'adam ba, ko da yake a baya mun taba duban Almasihu a haka. Amma yanzu mun daina shar'anta kowa ta haka.
17 Derfor, dersom nogen er i Kristus, da er han en ny skapning; det gamle er forganget, se, alt er blitt nytt!
Saboda haka, duk wanda ke cikin Almasihu, sabon halitta ne. Tsofaffin al'amura sun shude. Duba, sun zama sababbi.
18 Men alt dette er av Gud, som forlikte oss med sig selv ved Kristus og gav oss forlikelsens tjeneste,
Dukan wadannan abubuwa daga Allah ne. Ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu hidimar sulhu.
19 fordi Gud i Kristus forlikte verden med sig selv, så han ikke tilregner dem deres overtredelser og har nedlagt i oss ordet om forlikelsen.
Wato, cikin Almasihu, Allah na sulhunta duniya zuwa gare shi, ba tare da lissafin zunubansu a kansu ba. Yana damka mana sakon sulhu.
20 Så er vi da sendebud i Kristi sted, som om Gud selv formante ved oss; vi ber i Kristi sted: La eder forlike med Gud!
Don haka an zabe mu a matsayin wakilan Almasihu, kamar dai Allah na kira ga mutane ta wurin mu. Muna rokon ku, saboda Almasihu: ''ku sulhuntu ga Allah!''
21 Ham som ikke visste av synd, har han gjort til synd for oss, forat vi i ham skal bli rettferdige for Gud.
Shi ya maida Almasihu ya zama hadaya domin zunubinmu. Shine wanda bai taba zunubi ba. Ya yi haka ne don mu zama adalchin Allah a cikin sa.

< 2 Korintierne 5 >