< 2 Korintierne 5 >

1 For vi vet at om vårt legemes jordiske hus nedbrytes, så har vi en bygning av Gud, et hus som ikke er gjort med hender, evig i himlene. (aiōnios g166)
Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios g166)
2 For også mens vi er her til huse, sukker vi, fordi vi lenges efter å overklædes med vår bolig fra himmelen,
Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
3 så sant vi skal bli funnet iklædd, ikke nakne.
don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
4 For vi som er i denne hytte, sukker under byrden, fordi vi ikke vil avklædes, men overklædes, forat det dødelige kan bli opslukt av livet.
Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
5 Men den som har satt oss i stand just til dette, er Gud, han som og har gitt oss Ånden til pant.
Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
6 Derfor er vi alltid frimodige og vet at så lenge vi er hjemme i legemet, er vi borte fra Herren;
Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
7 for vi vandrer i tro, ikke i beskuelse;
Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
8 vi er altså frimodige, og vil heller være borte fra legemet og være hjemme hos Herren.
Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
9 Derfor setter vi og vår ære i, enten vi er hjemme eller borte, å tekkes ham.
Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
10 For vi skal alle åpenbares for Kristi domstol, forat enhver kan få igjen det som er skjedd ved legemet, efter det som han har gjort, enten godt eller ondt.
Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
11 Da vi altså kjenner frykten for Herren, søker vi å vinne mennesker, men for Gud er vi åpenbare; jeg håper og å være åpenbar for eders samvittigheter.
To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
12 Vi gir oss nu ikke atter skussmål for eder; men vi gir eder leilighet til å rose eder av oss, forat I kan ha noget å sette imot dem som roser sig av det de er i det utvortes og ikke i hjertet.
Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
13 For om vi er fra oss selv, da er det for Gud, og om vi er ved sans og samling, da er det for eder.
In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
14 For Kristi kjærlighet tvinger oss,
Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
15 idet vi har opgjort dette med oss selv at én er død for alle, derfor er de alle død; og han døde for alle, forat de som lever, ikke lenger skal leve for sig selv, men for ham som er død og opstanden for dem.
Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
16 Derfor kjenner vi fra nu av ikke nogen efter kjødet; har vi og kjent Kristus efter kjødet, så kjenner vi ham dog nu ikke lenger således.
Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
17 Derfor, dersom nogen er i Kristus, da er han en ny skapning; det gamle er forganget, se, alt er blitt nytt!
Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
18 Men alt dette er av Gud, som forlikte oss med sig selv ved Kristus og gav oss forlikelsens tjeneste,
Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
19 fordi Gud i Kristus forlikte verden med sig selv, så han ikke tilregner dem deres overtredelser og har nedlagt i oss ordet om forlikelsen.
wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
20 Så er vi da sendebud i Kristi sted, som om Gud selv formante ved oss; vi ber i Kristi sted: La eder forlike med Gud!
Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
21 Ham som ikke visste av synd, har han gjort til synd for oss, forat vi i ham skal bli rettferdige for Gud.
Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.

< 2 Korintierne 5 >