< 1 Kongebok 1 >

1 Nu var kong David gammel og høit til års, og de dekket ham til med tepper, men han kunde ikke bli varm.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Da sa hans tjenere til ham: En skulde lete efter en ung pike for min herre kongen, en jomfru som kan stelle for kongen og pleie ham og ligge i din favn, så min herre kongen blir varm.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 Så lette de i hele Israels land efter en vakker pike, og de fant Abisag fra Sunem og førte henne til kongen.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Det var en meget vakker pike; hun pleide kongen og tjente ham, men kongen hadde ikke omgang med henne.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Men Adonja, sønn til Haggit, gjorde sig høie tanker og sa: Jeg vil være konge. Og han fikk sig vogner og hestfolk og femti mann som løp foran ham.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Hans far hadde aldri i hans liv talt hårdt til ham og sagt: Hvorfor har du gjort dette? Han var og meget fager, og han var født næst efter Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Han samrådde sig med Joab, Serujas sønn, og med presten Abjatar, og de holdt med Adonja og hjalp ham.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 Men presten Sadok og Benaja, Jojadas sønn, og profeten Natan og Sime'i og Re'i og de helter David hadde, var ikke med Adonja.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Adonja slaktet får og okser og gjøkalver ved Sohelet-stenen, som er ved En-Rogel, og han innbød alle sine brødre, kongens sønner, og alle Judas menn som var i kongens tjeneste.
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 Men profeten Natan og Benaja og heltene og sin bror Salomo innbød han ikke.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Da sa Natan til Batseba, Salomos mor: Du har vel hørt at Adonja, Haggits sønn, er blitt konge, og vår herre David vet ikke noget om det?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 La mig nu få gi dig et råd, så du kan redde både ditt eget og din sønn Salomos liv!
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Gå inn til kong David og si til ham: Har du ikke, herre konge, med ed lovt din tjenerinne: Salomo, din sønn, skal være konge efter mig; han skal sitte på min trone? Hvorledes er det da gått til at Adonja er blitt konge?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Og mens du ennu er der inne og taler med kongen, skal jeg og komme inn og stadfeste dine ord.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 Da gikk Batseba inn til kongen i kammeret. Kongen var nu meget gammel, og Abisag fra Sunem tjente ham.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 Og Batseba bøide sig og kastet sig ned for kongen, og kongen sa: Hvad vil du?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 Hun svarte: Min herre! Du har tilsvoret din tjenerinne ved Herren din Gud: Salomo, din sønn, skal bli konge efter mig; han skal sitte på min trone.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Men se, nu er Adonja blitt konge, og du, herre konge, vet ikke noget om det.
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 Han har slaktet okser og gjøkalver og får i mengdevis og innbudt alle kongens sønner og presten Abjatar og hærføreren Joab; men Salomo, din tjener, har han ikke innbudt.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 Og nu, herre konge, er hele Israels øine vendt mot dig, forat du skal la dem vite hvem som skal sitte på min herre kongens trone efter ham.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Ellers kan det gå så at når min herre kongen ligger hos sine fedre, kommer jeg og min sønn Salomo til å holdes for forbrytere.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 Mens hun ennu talte med kongen, kom profeten Natan.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 Da blev det meldt kongen: Profeten Natan er her. Og han kom inn og trådte frem for kongen og kastet sig på sitt ansikt til jorden for ham.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Og Natan sa: Herre konge! Du har vel sagt: Adonja skal være konge efter mig, og han skal sitte på min trone?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 For han har idag draget ned og har slaktet okser og gjøkalver og får i mengdevis og innbudt alle kongens sønner og hærførerne og presten Abjatar, og nu eter og drikker de med ham og roper: Leve kong Adonja!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 Men mig, din tjener, og presten Sadok og Benaja, Jojadas sønn, og Salomo, din tjener, har han ikke innbudt.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Skulde dette være gjort på min herre kongens bud uten at du har latt dine tjenere vite hvem som skal sitte på min herre kongens trone efter ham?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Da tok kong David til orde og sa: Kall Batseba inn til mig! Og hun kom inn og trådte frem for kongen.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 Og kongen svor og sa: Så sant Herren lever, han som har utfridd mig fra all trengsel:
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Som jeg har tilsvoret dig ved Herren, Israels Gud: Salomo, din sønn, skal være konge efter mig, og han skal sitte på min trone i mitt sted, så vil jeg gjøre på denne dag.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Da bøide Batseba sig med ansiktet mot jorden og kastet sig ned for kongen og sa: Min herre kong David leve evindelig!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Og kong David sa: Kall hit til mig presten Sadok og profeten Natan og Benaja, Jojadas sønn! Og de kom inn og trådte frem for kongen.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Kongen sa til dem: Ta eders herres tjenere med eder og la min sønn Salomo ride på mitt eget muldyr og før ham ned til Gihon!
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 Der skal presten Sadok og profeten Natan salve ham til konge over Israel, og I skal støte i basunen og rope: Leve kong Salomo!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Så skal I følge ham hit op, og når han kommer, skal han sette sig på min trone, og han skal være konge i mitt sted; det er ham jeg har utsett til fyrste over Israel og Juda.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Da tok Benaja, Jojadas sønn, til orde og sa til kongen: Så være det! Måtte også Herren, min herre kongens Gud, ville det så!
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 Som Herren har vært med min herre kongen, så være han med Salomo og gjøre hans trone ennu større enn min herres, kong Davids trone!
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Da drog presten Sadok og profeten Natan og Benaja, Jojadas sønn, og livvakten ned, og de lot Salomo ride på kong Davids muldyr og førte ham til Gihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Og presten Sadok hentet oljehornet fra teltet og salvet Salomo; og de støtte i basunen, og alt folket ropte: Leve kong Salomo!
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 Og alt folket drog op efter ham, og de blåste på fløiter og jublet så høit at jorden revnet ved deres rop.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Dette hørte Adonja og alle de gjester som var hos ham; de var da nettop ferdig med å ete. Og da Joab hørte basunlyden, sa han: Hvorfor er det slik larm og bulder i byen?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 Mens han ennu talte, kom Jonatan, presten Abjatars sønn; og Adonja sa: Kom hit! Du er en bra mann og kommer visst med gode tidender.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Men Jonatan svarte og sa til Adonja: Nei! Vår herre kong David har gjort Salomo til konge.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 Kongen sendte med ham presten Sadok og profeten Natan og Benaja, Jojadas sønn, og livvakten, og de lot ham ride på kongens muldyr.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 Og presten Sadok og profeten Natan salvet ham til konge i Gihon, og så drog de op derfra i glede, og hele byen er i et røre. Det er den larm I hørte.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Og Salomo har også alt satt sig på kongetronen,
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 og kongens tjenere er kommet og har ønsket vår herre kong David til lykke og sagt: Din Gud la Salomos navn bli ennu herligere enn ditt navn og hans trone ennu større enn din trone! Og kongen tilbad på sitt leie.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Kongen har også sagt så: Lovet være Herren, Israels Gud, som idag har laget det så at det sitter en på min trone, så jeg har fått se det med egne øine!
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Da blev alle Adonjas gjester forferdet; de stod op og gikk, hver sin vei.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Adonja var redd Salomo; han stod op og gikk avsted og grep fatt i alterets horn.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 Da blev det meldt Salomo: Adonja er redd kong Salomo, og nu har han grepet fatt i alterets horn og sier: Kong Salomo må ennu idag tilsverge mig at han ikke vil la sin tjener dø for sverdet!
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Da sa Salomo: Vil han være en bra mann, skal det ikke falle et hår av hans hode til jorden; men blir det funnet noget ondt hos ham, skal han dø.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Så sendte kong Salomo folk avsted, og de førte ham ned fra alteret, og han kom og kastet sig ned for kong Salomo, og Salomo sa til ham: Gå hjem til ditt hus!
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Kongebok 1 >