< 1 Kongebok 20 >

1 Kongen i Syria Benhadad samlet hele sin hær, og to og tretti konger fulgte ham med hester og vogner; og han drog op og kringsatte Samaria og stred mot det.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Og han sendte bud inn i byen til Akab, Israels konge,
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 og lot si til ham: Så sier Benhadad: Ditt sølv og ditt gull hører mig til, og de vakreste av dine hustruer og barn hører og mig til.
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 Israels konge svarte og sa: Det er som du sier, min herre konge! Jeg og alt hvad mitt er, hører dig til.
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 Men sendebudene kom igjen og sa: Så sier Benhadad: Jeg sendte bud til dig og lot si: Ditt sølv og ditt gull og dine hustruer og dine barn skal du gi mig.
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 Men imorgen ved denne tid sender jeg mine tjenere til dig, og de skal ransake ditt hus og dine tjeneres huser, og alt som er dine øines lyst, skal de ta og føre bort med sig.
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 Da kalte Israels konge alle landets eldste til sig og sa: Nu ser I vel grant at han bare vil oss ondt! Han sendte bud til mig og krevde mine hustruer og mine barn, mitt sølv og mitt gull, og jeg nektet ham det ikke.
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 Da sa alle de eldste og alt folket til ham: Du må ikke høre på ham og ikke gi efter.
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 Så sa han til Benhadads sendebud: Si til min herre kongen: Alt det du første gang sendte bud til din tjener om, vil jeg gjøre; men dette kan jeg ikke gjøre. Med dette svar vendte sendebudene tilbake til ham.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 Da sendte Benhadad atter bud til ham og lot si: Gudene la det gå mig ille både nu og siden om Samarias støv skal kunne fylle nevene på alt det folk som er i mitt følge.
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 Da svarte Israels konge og sa: Si til ham: Ikke skulde den som binder sverdet om sig, rose sig lik den som løser det av sig!
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Da Benhadad hørte dette svar, mens han selv og kongene satt og drakk i løvhyttene, sa han til sine menn: Still eder op! Og de stilte sig op imot byen.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 Da trådte en profet frem til Akab, Israels konge, og sa: Så sier Herren: Ser du hele denne store mengde? Jeg gir den idag i din hånd, og du skal kjenne at jeg er Herren.
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Akab spurte: Ved hvem? Han svarte: Så sier Herren: Ved landshøvdingenes menn. Så spurte han: Hvem skal begynne striden? Han svarte: Du selv.
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 Så mønstret han landshøvdingenes menn, og de var to hundre og to og tretti; og efter dem mønstret han alt folket - alle Israels barn - syv tusen mann.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 De drog ut om middagen, mens Benhadad satt og drakk sig drukken i løvhyttene med de to og tretti konger som var kommet ham til hjelp.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 Landshøvdingenes menn drog først ut; Benhadad sendte folk ut for å speide, og de meldte ham at det hadde draget krigsfolk ut fra Samaria.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 Da sa han: Enten de har draget ut i fredelig øiemed, eller de har draget ut til strid, så grip dem levende!
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 Så drog de da ut fra byen, landshøvdingenes menn og hæren som fulgte dem,
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 og de hugg ned hver sin mann; syrerne flyktet, og Israel forfulgte dem; og Benhadad, kongen i Syria, slapp unda på en hest sammen med nogen ryttere.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Så drog Israels konge ut og slo hestene og stridsvognene og voldte et stort mannefall blandt syrerne.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 Da trådte profeten frem til Israels konge og sa til ham: Gå nu i gang med å ruste dig og tenk vel over hvad du skal gjøre! For til næste år vil kongen i Syria igjen dra op imot dig.
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 Men syrerkongens tjenere sa til ham: Deres guder er fjellguder, derfor vant de over oss; men strider vi med dem på sletten, da vinner vi sikkert over dem.
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 Gjør nu således: Avsett kongene, hver fra sin plass, og sett stattholdere i deres sted!
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Og få dig så selv en hær som er like så stor som den du mistet, og like så mange hester og vogner, og la oss så stride med dem på sletten! Da vinner vi sikkert over dem. Og han lyttet til deres råd og gjorde så.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 Året efter mønstret Benhadad syrerne og drog frem til Afek for å stride mot Israel.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 Og Israels barn blev mønstret og forsynt med levnetsmidler og drog ut imot dem; og Israels barn leiret sig midt imot dem som to små gjeteflokker, men syrerne opfylte landet.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 Da trådte den Guds mann frem og sa til Israels konge: Så sier Herren, sa han: Fordi syrerne har sagt: Herren er en fjellgud og ikke en dalgud, så vil jeg gi hele denne store mengde i din hånd, og I skal kjenne at jeg er Herren.
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 Så lå de nu i leir midt imot hverandre i syv dager. På den syvende dag kom det til strid, og Israels barn hugg på én dag ned hundre tusen mann fotfolk av syrerne.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 Og de som blev tilbake, flyktet til Afek og inn i byen; men muren falt ned over de syv og tyve tusen mann som var blitt tilbake. Benhadad flyktet også og kom inn i byen og sprang fra kammer til kammer.
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 Da sa hans tjenere til ham: Vi har hørt at kongene av Israels hus er milde konger; la oss legge sekk om våre lender og rep om våre hoder og gå ut til Israels konge! Kanskje han lar dig få leve!
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 Så bandt de sekk om sine lender og rep om sine hoder, og da de kom til Israels konge, sa de: Din tjener Benhadad sier: La mig få leve! Han svarte: Er han ennu i live? Han er min bror.
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Mennene tok dette for et godt varsel, og de søkte straks å få et ord fra ham som kunde vise om han mente det så, og de sa: Ja, Benhadad er din bror. Da sa han: Gå og hent ham! Så kom Benhadad ut til ham, og han lot ham stige op i sin vogn.
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Og Benhadad sa til ham: De byer som min far tok fra din far, vil jeg gi tilbake, og du kan gjøre dig gater i Damaskus, likesom min far gjorde i Samaria. Og jeg sa Akab vil på det vilkår gi dig fri. Så inngikk han et forbund med ham og gav ham fri.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Men en av profetenes disipler sa på Herrens bud til en annen: Slå mig! Men mannen vilde ikke slå ham.
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 Da sa han til ham: Fordi du ikke lød Herrens røst, så skal en løve drepe dig, når du går bort fra mig. Og da han gikk fra ham, kom en løve imot ham og drepte ham.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Så møtte han en annen mann og sa: Slå mig! Og mannen slo ham så han blev såret.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Derefter gikk profeten og stilte sig på veien for å møte kongen; men han gjorde sig ukjennelig ved å legge et bind over sine øine.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 Da nu kongen kom forbi, ropte han til kongen: Din tjener hadde draget ut og var med i striden; men i det samme kom det en mann frem som førte en annen mann til mig og sa: Ta vare på denne mann! Blir han borte, skal ditt liv trede i stedet for hans liv, eller også skal du betale mig en talent sølv.
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 Men din tjener hadde noget å gjøre her og der, og så blev mannen borte. Da sa Israels konge til ham: Du har din dom; du har selv felt den.
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 Da skyndte han sig og tok bindet fra øinene, og Israels konge kjente ham og så at han var en av profetene.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 Profeten sa til ham: Så sier Herren: Fordi du lot den mann som jeg hadde lyst i bann, slippe dig av hendene, så skal ditt liv trede i stedet for hans liv og ditt folk i stedet for hans folk.
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 Så drog Israels konge hjem mismodig og harm og kom til Samaria.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.

< 1 Kongebok 20 >