< 1 Kongebok 13 >

1 Men da kom det på Herrens bud en Guds mann til Betel fra Juda, nettop som Jeroboam stod ved alteret for å brenne røkelse.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 Og han ropte på Herrens bud mot alteret: Alter! Alter! Så sier Herren: Det skal fødes en sønn for Davids hus, Josias skal han hete, og på dig skal han ofre offerhaugenes prester, som brenner røkelse på dig, og det skal brennes menneskeben på dig.
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 På samme tid forkynte han et tegn og sa: Dette er tegnet på at Herren har talt: Alteret skal revne, og asken som er på det, skal spredes.
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 Da kong Jeroboam hørte de ord som den Guds mann ropte mot alteret i Betel, rakte han ut sin hånd fra alteret og sa: Grip ham! Men hånden som han rakte ut mot ham, visnet, og han kunde ikke dra den til sig igjen.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 Og alteret revnet, og asken spredtes fra alteret; det var det tegn som den Guds mann hadde forkynt på Herrens bud.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Da tok kongen til orde og sa til den Guds mann: Bønnfall Herren din Gud og bed for mig at jeg må kunne dra min hånd til mig igjen! Og den Guds mann bønnfalt Herren, og kongen kunde dra sin hånd til sig igjen - den blev som den hadde vært før.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 Da sa kongen til den Guds mann: Kom hjem med mig og vederkveg dig og la mig få gi dig en gave!
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 Men den Guds mann sa til kongen: Om du gav mig halvdelen av ditt hus, vilde jeg dog ikke gå hjem til dig; på dette sted vil jeg hverken ete brød eller drikke vann.
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 For dette bud fikk jeg av Herren: Du skal hverken ete brød eller drikke vann, og du skal ikke vende tilbake den vei du gikk.
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 Så tok han avsted en annen vei og vendte ikke tilbake den vei han var kommet til Betel.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 I Betel bodde det en gammel profet; hans sønn kom og fortalte ham alt det som den Guds mann den dag hadde gjort i Betel, og de ord han hadde talt til kongen. Da de hadde fortalt sin far dette,
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 spurte han dem: Hvad vei tok han? For hans sønner hadde sett hvad vei han hadde tatt den Guds mann som var kommet fra Juda.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 Da sa han til sine sønner: Sal asenet for mig! Så salte de asenet for ham, og han satte sig på det
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 og red avsted efter den Guds mann. Han fant ham sittende under en terebinte, og han sa til ham: Er du den Guds mann som er kommet fra Juda? Han svarte: Ja, det er jeg.
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Da sa han til ham: Kom hjem med mig og få dig litt mat!
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 Men han sa: Jeg kan ikke vende tilbake med dig og komme hjem til dig; jeg vil hverken ete brød eller drikke vann med dig på dette sted.
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 For det kom et ord til mig fra Herren: Du skal hverken ete brød eller drikke vann der; du skal ikke gå tilbake den vei du gikk.
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 Da sa han til ham: Jeg er også en profet likesom du, og en engel har talt et ord til mig fra Herren og sagt: Få ham med dig tilbake til ditt hus, så han kan få sig mat og drikke! Men da han sa det, løi han for ham.
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 Så vendte han da tilbake med ham og åt og drakk i hans hus.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 Men mens de satt til bords, kom Herrens ord til den profet som hadde fått ham med sig tilbake,
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 og han ropte til den Guds mann som var kommet fra Juda: Så sier Herren: Fordi du var gjenstridig mot Herrens ord og ikke holdt det bud Herren din Gud gav dig,
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 men vendte tilbake og åt og drakk på det sted hvorom han hadde sagt til dig: Du skal hverken ete brød eller drikke vann der, så skal ditt lik ikke komme i dine fedres grav.
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 Da han nu hadde ett og drukket, salte han asenet for ham - for profeten som han hadde fått med sig tilbake.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 Og han tok avsted; men på veien kom en løve imot ham og drepte ham; og hans lik lå slengt bortefter veien, og asenet stod ved siden av det og løven stod også ved siden av liket.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 Da fór det nogen menn forbi; de så liket som lå slengt bortefter veien, og løven som stod ved siden av liket; og da de kom til den by hvor den gamle profet bodde, fortalte de det der.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 Da profeten som hadde fått ham med tilbake fra veien, hørte det, sa han: Det er den Guds mann som var gjenstridig mot Herrens ord; derfor har Herren gitt ham i løvens vold, og den har sønderrevet ham og drept ham efter det ord som Herren hadde talt til ham.
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 Derefter sa han til sine sønner: Sal asenet for mig: Så salte de det.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 Og han tok avsted og fant hans lik slengt bortefter veien og asenet og løven stående ved siden av liket; løven hadde ikke fortært liket og heller ikke sønderrevet asenet.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 Da tok profeten op liket av den Guds mann og la ham på asenet og førte ham tilbake; og den gamle profet gikk inn i sin by for å holde sørgehøitid over ham og begrave ham.
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 Han la hans lik i sin egen grav, og de holdt sørgehøitid over ham og ropte: Ve, min bror!
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 Da han nu hadde begravet ham, sa han til sine sønner: Når jeg dør, skal I begrave mig i den grav hvor den Guds mann ligger begravet; I skal legge mine ben ved siden av hans ben.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 For det ord skal gå i opfyllelse som han på Herrens bud ropte mot alteret i Betel og mot alle offerhaugenes helligdommer i Samarias byer.
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Men heller ikke efter dette vendte Jeroboam om fra sin onde vei, men blev ved å gjøre hvem han vilde av folket til prester ved offerhaugene; han fylte alle deres hender som hadde lyst dertil, så de blev prester ved haugene.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 Og dette blev årsak til synd for Jeroboams hus og til at det blev utryddet og utslettet av jorden.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.

< 1 Kongebok 13 >