< Luka 16 >

1 Yesu atibabakiya kae benepunzi bake, “Pabile ni mundu yumo tajiri abile ni meneja, ni apeilwe habari ya kwamba meneja yono atapanya mali yake.
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 Nga nyoo tajiri atikumkema, nikum'bakiya, “nga namani yeni yaniipekania kunani yako? Upiye hesabu ya umeneja wako, kwa kuwa uwecha kwaa panga wameneja kae.”
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 Yolo meneja atibaya kumoyo wake, nipala panga namani, mana ngwana wango anikonyie kazi yango ya umeneja? Ntopo ngupu ywa lema, ni loba loba nibona oni.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 Nilitangite lanipala panga lenga panipoyelwa kukazi yango ya uwakili bandu banikaribishe kunyumba yabe.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 Nga nyoo wakili atikubakema adeni wa ngwana wake kila yumo akam'bakiye wa kwanza,'udaiwa kiasi gani ni ngwana wango?'
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 Atibaya ipimo mia jimo ya mauta akambakiya 'utole upesi hati yako utame upesi uyandike hamsini.'
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 Boka po atim'bakiya ywenge ni wenga udaiwa kiasi gani? 'atibaya 'ipimo mia jimo vya bwembe wa ngano, akam'bakiya,'utole hati yako uyandike themanini.'
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 Yolo ngwana atikumsifu meneja dhalimu cha pangite kwa weleu, kwa kuwa bana ba'kilambo wono ni werevu wanambone nashughulika kwa ung'anga ni bandu baupande wabe kuliko bababile bona banuru. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 Ni nenga nindakuwabakiya muipange ambwiga kwa mali ya udhalimu lenga baikosike babakaribishe katika makao ga milele. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 Ywa abiile mwaminifu katika lalibile lichunu muno upanga uaminifu katika likolo, ni abile dhalimu katika kichunu muno na katika kikolo pia.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 Mana mwenga mpangile kwaa uaminifu katika mali ya udhalimu ni ywako apalakukuamini katika mali ya kweli?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 Na mana mwabile kwaa baaminifu katika tumia mali ya mundu ywenge nyai ywapala kuwapea yaibile ya kwinu bene?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 Ntopo mtumishi ywaweza tumikia ngwana wanaibele, kwa maamna apala kumchukia yumo ni kumpenda ywenge, ama apala chikamana ni yolo ni kumdharau hayo. Hawesa kwaa kumtumikia Nnongo ni mali.”
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 Bai Mafarisayo, bababile apenda mbanje bayowine ago goti ni chalawa.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 Ni atiabakiya, “mwenga mwamuipunia haki nnonge ya bandu, lakini Nnongo aitangite mioyo yinu, kwa kuwa latitumikite kwa bandu upanga chukizo nnonge ya Nnongo.
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 Saliya na manabii vyabile mpaka Yohana paichile. Boka wakati wolo, habari njema ya ufalme wa Nnongo utitangazwa, ni kila mundu upaya jingya kwa ngupu.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 Lakini ni rahisi ka kumaunde ni pakilambo viboke kuliko hata herufi yimo ya saliyakosekana.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 Kila ywanneka nnyumbowe ni kobeka nnwawa ywenge azini, nayomkobeka ywembe ywalekwite ni nchengowe azini.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 Pabile ni mundu yumo tajiri awalite ngobo za rangi ya zambarau ni kitani safi ni abile atipurai kila lichoba utajiri wake nkolo.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 Ni maskini yumo lina lyake Lazaro abekitwe muligeti lyake, ni ana ilonda.
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 Ni ywembe atitamani yukuta kwa makombo yatambwike katika meza ya yolo tajiri hata mapwa waichile ni kumlambata ilonda yake.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 Ikawa yolo maskini awile ni tolekwa ni malaika mpaka pakiuba cha Ibrahimu. Yolo tajiri pia awile nachikwa.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 Ni kolo kumambe abile kumateso aobwile minyo gake ni kum'bona Ibrahimu kuutalu ni Lazalo pakiuba chake. (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 Atilela ni kubaya, Tate Ibrahimu, unihurumie unlei Lazaro achuye ncha ya lukonji lwake mumache, auburudishe ulimi wango, kwa sababu nindateswa katika mwoto wono.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 Lakini ibrahimu abayite, “mwana wango ukumbuke ya kwamba katika maisha yako utipokiya makowe yako mema, ni Lazaro nyo apatike mabaya. Ila nambeyambe abile pano anafarijiwa ni wenga unalumia.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 Ni zaidi ya ago, kubekitwe liembwa likolo ni lilacho kati yitu, lengo balo bapala boka kono icha kwoo kana bawechange wala bandu wa kwinu kana baloke icha kwitu.”
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 Yolo tajiri abayite,'nindakuloba tate Ibrahimu, kwamba umtume kunyumba ya tate bango.
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 kwa kuwa nibile nabo anunango atano linga abaonye, kwa hofu kwamba nabo baicha mahali pano nateseka.'
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 Lakini Ibrahimu abayite, “babile Musa ni manabii babapekani bao.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 Yolo tajiri atibaya, “nyoo kwaa, tate Ibrahimu, lakini mana ayendile mundu boka kono kwa wafu bapala tubu.'
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 Lakini Ibrahimu atikum'bakiya,'kana bakani kuwa pekania Musa ni manabii bapala shawishika kwaa ni mundu hata mana atiuluka boka mu'kiwo.
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luka 16 >