< URuthe 4 >

1 UBhowazi wasesenyukela esangweni, wahlala phansi lapho. Khangela-ke, kwedlula isihlobo esingumhlengi leso uBhowazi ayekhulume ngaso. Wasesithi: Phambuka uhlale phansi lapha, we zibanibani. Wasephambuka, wahlala phansi.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Wasethatha amadoda alitshumi ebadaleni bomuzi, wathi: Hlalani phansi lapha. Asehlala phansi.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Wasesithi kulesosihlobo esingumhlengi: Isiqinti sensimu esasingesomfowethu uElimeleki, uyasithengisa uNawomi, osebuyile evela elizweni lakoMowabi.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Ngakho mina ngithe: Ngikwembule endlebeni yakho ngisithi: Sithenge phambi kwabahlali laphambi kwabadala babantu bakithi. Uba uzasihlenga, sihlenge. Kodwa uba engekho ongasihlenga, ungitshele, ukuze ngazi; ngoba engekho ngaphandle kwakho ongasihlenga, mina-ke ngilandela wena. Wasesithi: Mina ngizasihlenga.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 UBhowazi wasesithi: Mhla uthenga insimu esandleni sikaNawomi, uzayithenga lakuRuthe umMowabikazi, umfazi womuyi, ukuze umise ibizo lomuyi elifeni lakhe.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Lesosihlobo esingumhlengi sasesisithi: Ngingeke ngazihlengela sona, hlezi ngone ilifa lami. Zihlengele wena ilungelo lami lokuhlenga, ngoba kangilamandla okuhlenga.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Lokhu-ke kwakukhona mandulo koIsrayeli mayelana lokuhlenga lokuntshintsha, ukuqinisa lonke udaba: umuntu akhiphe inyathela lakhe, alinike umakhelwane wakhe; lokhu-ke kwakuyibufakazi koIsrayeli.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Ngakho isihlobo esingumhlengi sathi kuBhowazi: Zithengele yona; sasesikhipha inyathela laso.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 UBhowazi wasesithi kubadala lakubo bonke abantu: Lingabafakazi lamuhla bokuthi ngithengile konke okwakungokukaElimeleki lakho konke okwakungokukaKiliyoni lokukaMaheloni esandleni sikaNawomi.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 LoRuthe laye umMowabikazi, umkaMaheloni, ngizithengele ukuze abe ngumkami, ukuze ngimise ibizo likamuyi elifeni lakhe, ukuze ibizo lomuyi lingaqunywa lisuke phakathi kwabafowabo lesangweni lendawo yakhe. Lingabafakazi lamuhla.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Bonke abantu ababesesangweni labadala basebesithi: Singabafakazi; kungathi iNkosi ingamenza lo owesifazana ongena endlini yakho abe njengoRasheli lanjengoLeya abakha bobabili indlu kaIsrayeli. Njalo wenze ngamandla eEfratha, uzenzele ibizo eBhethelehema,
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 lendlu yakho ibe njengendlu kaPerezi uTamari amzalela uJuda, ngenzalo iNkosi ezakunika yona ngalo owesifazana omutsha.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Ngakho uBhowazi wamthatha uRuthe, waba ngumkakhe; wasengena kuye, iNkosi yamnika ukuthi athathe isisu, wazala indodana.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Abesifazana basebesithi kuNawomi: Kayibusiswe iNkosi engakutshiyanga ungelaso isihlobo esingumhlengi lamuhla, ukuthi ibizo laso limenyezelwe koIsrayeli!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 Uzakuba kuwe ngumbuyisi wempilo lomondli wobudala bakho, ngoba umzele umalokazana wakho okuthandayo, ongcono kuwe kulamadodana ayisikhombisa.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 UNawomi wasemthatha umntwana, wamfaka esifubeni sakhe, waba ngumlizane wakhe.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 Omakhelwanekazi basebemutha ibizo besithi: Kulendodana ezalelwe uNawomi. Babiza ibizo layo uObedi; nguyise kaJese, uyise kaDavida.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Lalezi yizizukulwana zikaPerezi. UPerezi wazala uHezironi,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 uHezironi wasezala uRamu, uRamu wasezala uAminadaba,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 uAminadaba wasezala uNashoni, uNashoni wasezala uSalimoni,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 uSalimoni wasezala uBhowazi, uBhowazi wasezala uObedi,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 uObedi wasezala uJese, uJese wasezala uDavida.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< URuthe 4 >