< Amahubo 112 >

1 Dumisani iNkosi! Ubusisiwe umuntu oyesabayo iNkosi, othokoza kakhulu ngemithetho yayo.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 Inzalo yakhe izakuba lamandla emhlabeni; isizukulwana sabaqotho sizabusiswa.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Imfuyo lenotho kuzakuba sendlini yakhe, lokulunga kwakhe kuzakuma kuze kube nininini.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Kuyabaphumela abaqotho ukukhanya emnyameni; ilomusa lesihawu lokulunga.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 Umuntu olungileyo ngolesisa lowebolekisayo, wenza izindaba zakhe ngokulunga.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Ngoba kayikunyikinywa phakade; olungileyo uzakuba sekukhunjulweni kuze kube nininini.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Kayikwesaba umbiko omubi, inhliziyo yakhe iqinile, ithemba eNkosini.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 Isekelwe inhliziyo yakhe, kayikwesaba, aze abone isiloyiso sakhe phezu kwezitha zakhe.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Uhlakazile, uyabanika abayanga; ukulunga kwakhe kumi kuze kube nininini; uphondo lwakhe luzaphakanyiswa ngodumo.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 Omubi uyakubona, athukuthele; agedle amazinyo akhe, ancibilike; isifiso sababi sizabhubha.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Amahubo 112 >