< UMathewu 16 >

1 AbaFarisi labaSadusi sebezile, bemlinga bamcela ukuthi abatshengise isibonakaliso esivela ezulwini.
Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo don su gwada Yesu ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
2 Kodwa waphendula wathi kubo: Kusihlwa lithi: Umkhathi muhle; ngoba isibhakabhaka sibomvu;
Ya amsa ya ce, “Sa’ad da yamma ta yi, kukan ce, ‘Yanayi zai yi kyau, gama sararin sama ya yi ja,’
3 lekuseni lithi: Umkhathi mubi lamuhla; ngoba isibhakabhaka sibomvu sinyukubele. Bazenzisi, liyakwazi ukwehlukanisa umumo wesibhakabhaka; kodwa izibonakaliso zezikhathi lingeke yini?
da safe kuma, ku ce, ‘Yau kam za a yi hadari, gama sararin sama ya yi ja, ya kuma ɓata fuska.’ Kun san yadda za ku fassara yanayin sararin sama, amma ba kwa iya fassarar alamun lokuta.
4 Isizukulwana esibi lesifebayo sidinga isibonakaliso; kodwa kasiyikunikwa isibonakaliso, ngaphandle kwesibonakaliso sikaJona umprofethi. Wasebatshiya, wahamba.
Wannan mugu da mazinacin zamani yana neman wani abin banmamaki, amma ba wata alamar da za a nuna wa wannan zamani sai dai ta Yunana.” Sai Yesu ya bar su ya tafi abinsa.
5 Sebefikile ngaphetsheya abafundi bakhe babekhohliwe ukuthatha izinkwa.
Da suka ƙetare tafkin, almajiran sun manta su riƙe burodi.
6 UJesu wasesithi kubo: Nanzelelani liqaphele imvubelo yabaFarisi labaSadusi.
Yesu ya ce musu, “Ku yi hankali, ku yi taka zallan da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
7 Basebekhulumisana besithi: Ngoba singathathanga izinkwa.
Sai suka fara tattaunawa da junansu suna cewa, “Ko don ba mu kawo burodi ba ne.”
8 UJesu esekwazi wathi kubo: Lina abokholo oluncinyane, kungani likhulumisana ngokuthi alithathanga izinkwa?
Sane da abin da suke zance, sai Yesu ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da junanku a kan ba ku zo da burodi ba?
9 Kalikaqedisisi yini, futhi kalikhumbuli izinkwa ezinhlanu zenkulungwane ezinhlanu, lokuthi labutha izitsha ezingaki?
Har yanzu ba ku gane ba ne? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka tattara cike?
10 Futhi lezinkwa eziyisikhombisa zenkulungwane ezine, lokuthi labutha izitsha ezingaki?
Ko kuma burodi bakwai nan na mutum dubu huɗu, cikakku manyan kwanduna nawa kuka ɗauka?
11 Kaliqedisisi njani, ukuthi bekungemayelana lesinkwa ebengikukhuluma kini ukuthi liqaphele imvubelo yabaFarisi labaSadusi?
Yaya kuka kāsa gane cewa ba zancen burodi nake yi ba? Sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da Sadukiyawa.”
12 Basebeqedisisa ukuthi katshongo ukuthi baqaphele imvubelo yezinkwa, kodwa imfundiso yabaFarisi labaSadusi.
Sa’an nan suka gane ba cewa yake musu su yi hankali da yistin da ake amfani da shi a burodi ba ne, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da Sadukiyawa ne.
13 Kwathi uJesu esefikile kungxenye zeKesariya yeFiliphu wababuza abafundi bakhe, esithi: Abantu bathi, mina, iNdodana yomuntu, ngingubani?
Sa’ad da Yesu ya zo yankin Kaisariya Filibbi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke ce da Ɗan Mutum?”
14 Basebesithi: Abanye bathi: NguJohane uMbhabhathizi; labanye bathi: NguElija; labanye bathi: NguJeremiya, kumbe ngomunye wabaprofethi.
Suka amsa, “Waɗansu suna ce Yohanna Mai Baftisma; waɗansu kuma suna ce annabi Iliya; har wa yau waɗansu suna ce Irmiya ne ko kuma ɗaya daga cikin annabawa.”
15 Wathi kubo: Lina-ke lithi ngingubani?
Ya tambaye su, “Amma ku fa, wane ne ni a ganinku?”
16 USimoni Petro wasephendula wathi: Wena unguKristu, iNdodana kaNkulunkulu ophilayo.
Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Allah mai rai.”
17 UJesu wasephendula wathi kuye: Ubusisiwe, Simoni ndodana kaJona, ngoba inyama legazi kakukwembulelanga lokhu, kodwa uBaba osemazulwini.
Yesu ya amsa ya ce, “Mai albarka ne kai Siman ɗan Yunana, gama ba mutum ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin sama.
18 Lami-ke ngiyakutshela, ukuthi wena unguPetro; laphezu kwalelidwala ngizalakha ibandla lami, lamasango esihogo kawayikulehlula. (Hadēs g86)
Ina kuwa gaya maka, kai ne Bitrus, a kan wannan dutse zan gina ikkilisiyata, kuma ƙofofin Hadesba za su rinjaye ta ba. (Hadēs g86)
19 Futhi ngizakunika izihluthulelo zombuso wamazulu; njalo loba yini ozayibopha emhlabeni, izakuba ibotshiwe emazulwini; njalo loba yini ozayithukulula emhlabeni, izakuba ithukululwe emazulwini.
Zan ba ka mabuɗan mulkin sama; kome ka daure a duniya zai zama a daure a sama, kome kuma ka kunce a duniya zai zama a kunce a sama.”
20 Wasebalayisisa abafundi ukuthi bangatsheli muntu ukuthi yena unguJesu onguKristu.
Sa’an nan ya gargaɗe almajiransa cewa kada su faɗa wa kowa shi ne Kiristi.
21 Kusukela kulesosikhathi uJesu waqala ukubatshengisa abafundi bakhe ukuthi umele ukuya eJerusalema, njalo ahlupheke okunengi ngabadala labapristi abakhulu lababhali, abulawe, avuswe ngosuku lwesithathu.
Tun daga wannan lokaci Yesu ya fara bayyana wa almajiransa cewa dole yă tafi Urushalima yă sha wahaloli da yawa a hannun dattawa, manyan firistoci da kuma malaman dokoki, dole a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.
22 UPetro wasesiya laye eceleni waqala ukumkhuza esithi: Kakungabi kuwe, Nkosi; lokhu kakusoze kwenziwa kuwe.
Bitrus ya ja shi gefe ya fara tsawata masa yana cewa, “Sam, Ubangiji! Wannan ba zai taɓa faruwa da kai ba!”
23 Kodwa yena watshibilika wathi kuPetro: Suka ngemva kwami, Sathane, uyisikhubekiso kimi; ngoba kawucabangi izinto zikaNkulunkulu, kodwa ezabantu.
Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Rabu da ni, Shaiɗan! Kai abin sa tuntuɓe ne a gare ni; ba ka tunanin al’amuran Allah, sai dai al’amuran mutane.”
24 UJesu wasesithi kubafundi bakhe: Uba umuntu ethanda ukuza ngemva kwami, kazidele, athathe isiphambano sakhe, angilandele.
Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni.
25 Ngoba loba ngubani othanda ukusindisa impilo yakhe izamlahlekela; kodwa loba ngubani olahlekelwa yimpilo yakhe ngenxa yami uzayithola;
Gama duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi.
26 ngoba kuzamsizani umuntu nxa ezuza umhlaba wonke, kodwa alahlekelwe ngumphefumulo wakhe? Kumbe umuntu uzanikani kube lihlawulo lomphefumulo wakhe?
Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka, amma ya rasa ransa? Ko kuwa me mutum zai bayar a bakin ransa?
27 Ngoba iNdodana yomuntu izakuza ngenkazimulo kaYise kanye lengilosi zayo, khona izavuza ngulowo lalowo njengokwenza kwakhe.
Gama Ɗan Mutum zai zo cikin ɗaukakar Ubansa, tare da mala’ikunsa, sa’an nan zai ba wa kowane mutum lada gwargwadon abin da ya yi.
28 Ngiqinisile ngithi kini: Bakhona abanye kwabemiyo lapha, abangasoze bezwe ukufa, baze bayibone iNdodana yomuntu isiza embusweni wayo.
“Gaskiya nake gaya muku, akwai waɗansu da suke tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin mulkinsa.”

< UMathewu 16 >