< ULukha 1 >

1 Njengoba abanengi sebebeke izandla ukubeka ngendlela efaneleyo ukulandiswa kwezinto eziqiniseke ngokupheleleyo phakathi kwethu,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 njengalokhu basinika labo ababonayo ngamehlo ekuqaleni njalo bezinceku zelizwi,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 kukhanye kukuhle lakimi, sengizihlolisisile zonke izinto kusukela ekuqaleni, ukuthi ngikubhalele ngokulandelana, mhlekazi Teyofilu,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 ukuze wazi iqiniso ngalezozinto ozifundisiweyo.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Ensukwini zikaHerodi inkosi yeJudiya kwakukhona umpristi othile othiwa nguZakariya, oweqembu likaAbhiya; lomkakhe wayevela kumadodakazi kaAroni, lebizo lakhe linguElizabethi.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Njalo babelungile bobabili phambi kukaNkulunkulu, behamba ngayo yonke imilayo lezimiso zeNkosi, bengasoleki.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Njalo babengelamntwana, ngoba uElizabethi wayeyinyumba, basebeleminyaka eminengi bobabili.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Kwasekusithi esenza inkonzo yobupristi phambi kukaNkulunkulu esesimisweni seqembu lakibo,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 ngomkhuba wenkonzo yobupristi, nguye owadliwa yinkatho yokutshisa impepha esengene ethempelini leNkosi.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Njalo ixuku lonke labantu lalikhuleka ngaphandle ngesikhathi sokutshisa impepha.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Ingilosi yeNkosi yasibonakala kuye, imi ngakwesokunene selathi lempepha.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Kwathi uZakariya eyibona waqhuqha, lokwesaba kwawela phezu kwakhe.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Kodwa ingilosi yathi kuye: Ungesabi Zakariya; ngoba umkhuleko wakho uzwakele, lomkakho uElizabethi uzakuzalela indodana, njalo uzakuthi ibizo layo nguJohane.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Futhi uzakuba lenjabulo lentokozo, labanengi bazakujabulela ukuzalwa kwakhe.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Ngoba uzakuba mkhulu phambi kweNkosi, iwayini kanye lokunathwayo okulamandla kasoze akunathe, futhi uzagcwaliswa ngoMoya oNgcwele kusukela esesesiswini sikanina.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Labanengi kubantwana bakoIsrayeli uzabaphendulela eNkosini uNkulunkulu wabo;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 njalo yena uzahamba phambi kwayo emoyeni lemandleni kaElija, ukuphendulela inhliziyo zaboyise kubantwana, labangalaleliyo ekuhlakanipheni kwabalungileyo, ukulungiselela iNkosi isizwe esilungisiweyo.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 UZakariya wasesithi kuyo ingilosi: Ngizakwazi ngani lokhu? Ngoba mina ngilixhegu, lomkami useleminyaka eminengi.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Ingilosi yasiphendula yathi kuye: NginguGabriyeli mina, omayo phambi kukaNkulunkulu; njalo ngithunyiwe ukukhuluma lawe, lokukubikela lezizindaba ezinhle.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Njalo khangela, uzakuba yisimungulu njalo wehluleke ukukhuluma, kuze kube lusuku okuzakwenzeka ngalo lezizinto, ngenxa yokuthi ungakholwanga amazwi ami, azagcwaliseka ngesikhathi sawo.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Labantu babemlindele uZakariya; bamangala ngokuphuza kwakhe ethempelini.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Kuthe esephuma wehluleka ukukhuluma labo; njalo bazi ukuthi ubone umbono ethempelini; njalo yena wayesebaqhweba, wahlala eyisimungulu.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Kwasekusithi seziphelile insuku zokukhonza kwakhe, waya endlini yakhe.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Kwathi emva kwalezonsuku uElizabethi umkakhe wathatha isisu, wazifihla okwezinyanga ezinhlanu, esithi:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Yenze kanje kimi iNkosi ensukwini eyangikhangela ngazo ukususa ihlazo lami phakathi kwabantu.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Kwathi ngenyanga yesithupha ingilosi uGabriyeli yathunywa nguNkulunkulu emzini weGalili othiwa yiNazaretha,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 entombini eyayigane indoda, ebizo layo lalinguJosefa, eyendlu kaDavida; lebizo lentombi linguMariya.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Ingilosi yasingena kuye yathi: Ekuhle, wena othandiweyo! INkosi ilawe, ubusisiwe wena phakathi kwabesifazana.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Kwathi eseyibonile wethuswa kakhulu yilizwi layo, wanakana ukuthi yikubingelela okunjani lokhu.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Ingilosi yasisithi kuye: Ungesabi, Mariya; ngoba uthole uthando kuNkulunkulu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Njalo khangela, uzathatha isisu, uzale indodana, uzakuthi ibizo layo nguJesu.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Yena uzakuba mkhulu, uzabizwa ngokuthi yiNdodana yoPhezukonke; futhi iNkosi uNkulunkulu izamnika isihlalo sobukhosi sikayise uDavida,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 njalo uzabusa phezu kwendlu kaJakobe kuze kube nininini, langombuso wakhe kawuzukuba lokuphela. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 UMariya wasesithi kuyo ingilosi: Lokhu kungenzeka njani, njengoba ngingazi indoda?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ingilosi yasiphendula yathi kuye: UMoya oNgcwele uzakuza phezu kwakho, lamandla oPhezukonke azakwembesa; ngakho lalokhu okungcwele okuzazalwa nguwe kuzakuthiwa yiNdodana kaNkulunkulu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Njalo khangela, isinini sakho uElizabethi, laye ukhulelwe yindodana ebudaleni bakhe; lale yinyanga yesithupha kuye obekuthiwa uyinyumba.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Ngoba kuNkulunkulu kakulalutho oluzakwehlula.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 UMariya wasesithi: Khangela, incekukazi yeNkosi; kakube kimi njengelizwi lakho. Ingilosi yasisuka kuye.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Ngalezonsuku uMariya wasesukuma waya ezintabeni ngokuphangisa, emzini weJuda,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 wangena endlini kaZakariya, wabingelela uElizabethi.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Kwasekusithi uElizabethi ezwe ukubingelela kukaMariya, inkonyane yeqa esiswini sakhe; loElizabethi wagcwaliswa ngoMoya oNgcwele,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 wamemeza ngelizwi elikhulu, wathi: Ubusisiwe wena phakathi kwabesifazana, njalo sibusisiwe isithelo sesizalo sakho!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Kanti kuvela ngaphi lokhu kimi, ukuthi unina weNkosi yami eze kimi?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Ngoba khangela, kuthe ilizwi lokubingelela kwakho lifika endlebeni zami, umntwana weqa esiswini sami ngokuthokoza.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Futhi ubusisiwe okholiweyo, ngoba kuzagcwaliseka lezozinto ezakhulunywa kuye yiNkosi.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 UMariya wasesithi: Umphefumulo wami uyayikhulisa iNkosi,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 lomoya wami uyathokoza kuNkulunkulu uMsindisi wami,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 ngoba ukhangele ubuphansi bencekukazi yakhe. Ngoba khangela, kusukela khathesi zonke izizukulwana zizakuthi ngibusisiwe.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Ngoba yena olamandla ungenzele izinto ezinkulu, lingcwele lebizo lakhe,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 lesihawu sakhe sikusizukulwana ngesizukulwana kulabo abamesabayo.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Wenzile amandla ngengalo yakhe; uhlakazile abazigqajayo ekunakaneni kwenhliziyo zabo.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Wehlisile iziphathamandla ezihlalweni zobukhosi, kodwa uphakamisile abantukazana.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Abalambileyo ubasuthise ngezinto ezinhle, kodwa abanothileyo wabamukisa beze.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Umsizile uIsrayeli inceku yakhe, ngokukhumbula isihawu,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 njengoba watsho kubobaba bethu, kuAbrahama, lenzalweni yakhe kuze kube nininini. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 UMariya wasehlala laye okungaba zinyanga ezintathu, wasebuyela endlini yakhe.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Isikhathi sikaElizabethi sokuthi abelethe sesiphelele, wasebeletha indodana.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Abakhelene laye lezinini zakhe basebesizwa ukuthi iNkosi yenze isihawu sayo saba sikhulu kuye, basebethokoza laye.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Kwasekusithi ngosuku lwesificaminwembili, beza ukuzasoka usane; balubiza ngebizo likayise ngokuthi nguZakariya.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Kodwa unina waphendula wathi: Hatshi bo, kodwa luzathiwa nguJohane.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Basebesithi kuye: Kakho ezihlotsheni zakho obizwa ngalelibizo.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Basebeqhweba uyise, ukuthi angathanda ukuthi lubizwe ngokuthini.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Wasecela into yokubhalela, wabhala, esithi: NguJohane ibizo lalo; basebemangala bonke.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Njalo wahle wavulwa umlomo wakhe lolimi lwakhe lwatshwaphululwa, wasekhuluma edumisa uNkulunkulu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Lokwesaba kwehlela phezu kwabo bonke abakhelene labo; njalo kwakhulunywa ngazo zonke lezizinto kulo lonke elezintabeni zeJudiya,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 labo bonke abazizwayo bazilondoloza ezinhliziyweni zabo, besithi: Kambe lolusane luzakuba njani? Njalo isandla seNkosi sasilalo.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 LoZakariya uyise wagcwaliswa ngoMoya oNgcwele, waprofetha, esithi:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Ibusisiwe iNkosi uNkulunkulu kaIsrayeli, ngoba ihambele yasenzela inkululeko isizwe sayo,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 yasivusela uphondo losindiso endlini kaDavida inceku yayo,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 njengalokho yakhuluma ngomlomo wabaprofethi bayo abangcwele kusukela ekuqaleni komhlaba, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 isikhulula ezitheni zethu, lesandleni sabo bonke abasizondayo;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 ukwenzela obaba bethu isihawu, lokukhumbula isivumelwano sayo esingcwele,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 isifungo eyasifunga kubaba wethu uAbrahama,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 ukusinika, ukuthi sesikhululiwe esandleni sezitha zethu, siyikhonze singelakwesaba,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 ngobungcwele langokulunga phambi kwayo zonke izinsuku zempilo yethu.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Lawe-ke, sane, uzabizwa ngokuthi ungumprofethi woPhezukonke; ngoba uzahamba phambi kobuso beNkosi ukulungisa izindlela zayo;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 lokunika isizwe sayo ulwazi losindiso ngothethelelo lwezono zabo,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 ngesihelo sikaNkulunkulu wethu, okuthi ngaso ukusa kwaphezulu kusethekelele,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 ukubakhanyisela abahlezi emnyameni lethunzini lokufa, ukuqondisa inyawo zethu endleleni yokuthula.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Wakhula-ke umntwana omncane, waqina emoyeni, waba sezinkangala kwaze kwaba lusuku lokubonakala kwakhe kuIsrayeli.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< ULukha 1 >