< 2 Amakhosi 13 >

1 Ngomnyaka wamatshumi amabili lantathu kaJowashi indodana kaAhaziya inkosi yakoJuda uJehowahazi indodana kaJehu waba yinkosi phezu kukaIsrayeli eSamariya, wabusa iminyaka elitshumi lesikhombisa.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 Wenza okubi emehlweni eNkosi, walandela izono zikaJerobhowamu indodana kaNebati owenza uIsrayeli one, kasukanga kuzo.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 Ulaka lweNkosi lwaselumvuthela uIsrayeli, yabanikela esandleni sikaHazayeli inkosi yeSiriya lesandleni sikaBenihadadi indodana kaHazayeli, zonke lezonsuku.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 UJehowahazi wasencenga ubuso beNkosi, iNkosi yamuzwa, ngoba yabona incindezelo kaIsrayeli, ngoba inkosi yeSiriya yabacindezela.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 (INkosi yasisipha uIsrayeli umsindisi ukuze baphume ngaphansi kwesandla samaSiriya; abantwana bakoIsrayeli basebehlala emathenteni abo njengakuqala.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Loba kunjalo kabasukanga ezonweni zendlu kaJerobhowamu owenza uIsrayeli one, bahamba kuzo; lesixuku laso sasilokhu siseSamariya.)
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Ngoba kayimtshiyelanga uJehowahazi abantu, kuphela abagadi bamabhiza abangamatshumi amahlanu, lenqola ezilitshumi, labahamba ngenyawo abazinkulungwane ezilitshumi; ngoba inkosi yeSiriya yayibabhubhisile, yabenza baba njengothuli ngokubhula.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Ezinye-ke zezindaba zikaJehowahazi, lakho konke akwenzayo, lamandla akhe, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoIsrayeli?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 UJehowahazi waselala laboyise, bamngcwabela eSamariya; uJowashi indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 Ngomnyaka wamatshumi amathathu lesikhombisa kaJowashi inkosi yakoJuda uJehowashi indodana kaJehowahazi waba yinkosi phezu kukaIsrayeli eSamariya; wabusa iminyaka elitshumi lesithupha.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 Laye wenza okubi emehlweni eNkosi, kasukanga ezonweni zonke zikaJerobhowamu indodana kaNebati owenza uIsrayeli one; wahamba kuzo.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 Ezinye-ke zezindaba zikaJowashi, lakho konke akwenzayo, lamandla akhe alwa ngawo loAmaziya inkosi yakoJuda, kakubhalwanga yini egwalweni lwemilando yamakhosi akoIsrayeli?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 UJowashi waselala laboyise, uJerobhowamu wasehlala esihlalweni sakhe sobukhosi. UJowashi wangcwatshelwa eSamariya lamakhosi akoIsrayeli.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 UElisha wasegula umkhuhlane wakhe afa ngawo; uJowashi inkosi yakoIsrayeli wasesehlela kuye, wakhala inyembezi phezu kobuso bakhe, wathi: Baba wami! Baba wami! Nqola yakoIsrayeli lamabhiza ayo!
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 UElisha wasesithi kuye: Thatha idandili lemitshoko. Wasezithathela idandili lemitshoko.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Wasesithi enkosini yakoIsrayeli: Beka isandla sakho edandilini. Wasesibeka isandla sakhe. UElisha wasebeka izandla zakhe phezu kwezandla zenkosi.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Wasesithi: Vula iwindi ngempumalanga. Yasilivula. UElisha wasesithi: Tshoka! Yasitshoka. Wasesithi: Umtshoko wenkululeko yeNkosi, lomtshoko wenkululeko kuSiriya. Ngoba uzatshaya amaSiriya eAfeki uze uwaqede.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Wasesithi: Thatha imitshoko. Yasiyithatha. Wasesithi enkosini yakoIsrayeli: Tshaya emhlabathini. Yasitshaya kathathu, yasisima.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Umuntu kaNkulunkulu waseyithukuthelela, wathi: Ngabe utshaye kahlanu kumbe kasithupha, ngakho ubuzayitshaya iSiriya uze uyiqede; khathesi-ke uzatshaya iSiriya kathathu kuphela.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 UElisha wasesifa, basebemngcwaba. Amaviyo amaMowabi asengena elizweni ekuthwaseni komnyaka.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 Kwasekusithi bengcwaba umuntu, khangela-ke, babona iviyo, baphosela lowomuntu engcwabeni likaElisha. Kwathi umuntu esiyathinta amathambo kaElisha waphila, wasukuma wema ngenyawo.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 UHazayeli inkosi yeSiriya wasecindezela uIsrayeli insuku zonke zikaJehowahazi.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 INkosi yasisiba lomusa kibo, yaba lesihawu kubo, yaphendukela kibo ngenxa yesivumelwano sayo loAbrahama, uIsaka, loJakobe, kayithandanga ukubabhubhisa, kayibaxotshanga ebusweni bayo kuze kube khathesi.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 UHazayeli inkosi yeSiriya wasesifa; uBenihadadi indodana yakhe wasesiba yinkosi esikhundleni sakhe.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 UJehowashi indodana kaJehowahazi wasebuya wathatha imizi esandleni sikaBenihadadi indodana kaHazayeli owayeyithethe esandleni sikaJehowahazi uyise ngempi. UJowashi wamtshaya kathathu, waseyibuyisela imizi yakoIsrayeli.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Amakhosi 13 >