< ULukha 21 >

1 UJesu wathi ekhangela wabona izinothi zifaka iminikelo yazo esitsheni somnikelo.
Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
2 Wabona njalo umfelokazi ongumyanga efaka okuzinhlamvana kwethusi okubili.
Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
3 Wathi, “Ngilitshela iqiniso ngithi umfelokazi lo ongumyanga unikele okudlula bonke abanye.
Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
4 Bonke lababantu banikele izipho zabo ngokwenotho yabo, kodwa yena ebuyangeni bakhe ufake konke abelakho.”
Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
5 Abanye abafundi bakhe babekhulukhuluma ngokubalazwa kwethempeli ngamatshe amahle langezipho ezazinikelwe kuNkulunkulu. Kodwa uJesu wathi,
Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
6 “Mayelana lalokhu elikubona lapha, sizafika isikhathi lapho okungeyikutshiywa ilitshe phezu kwelinye; wonke azaphoselwa phansi.”
“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
7 Babuza bathi, “Mfundisi, izinto lezi zizakwenzakala nini? Njalo sizakuba yini isibonakaliso sokuthi sezizakwenzeka na?”
Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
8 Waphendula wathi, “Qaphelani lingakhohliswa. Ngoba abanengi bazakuza ngebizo lami besithi, ‘Nginguye,’ njalo bathi, ‘Isikhathi sesisondele.’ Lingabalandeli.
Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
9 Nxa lisizwa ngezimpi lezikhukhulambuso, lingethuki. Lezizinto kuzamele zenzeke kuqala, kodwa isiphetho kasizukufika ngalesosikhathi.”
Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
10 Wasesithi kubo: “Isizwe sizavukela isizwe, lombuso uvukele umbuso.
Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
11 Kuzakuba lokuzamazama komhlaba okukhulu, indlala lezifo ezindaweni ezinengi, izehlakalo ezesabekayo lezibonakaliso ezinengi zivela emkhathini.
Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
12 Kodwa kungakenzakali konke lokhu bazalibamba, balihlukuluze. Bazalinikela emasinagogweni baliphosele lasezintolongweni njalo lizamiswa phambi kwamakhosi lababusi ngenxa yebizo lami.
“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
13 Lokhu kuzalenza libe ngofakazi kimi.
Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
14 Kodwa bekani amaphaphu phansi, lingazihluphi ngokuthi lizazivikela lisithini.
Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
15 Ngoba ngizalinika amazwi lokuhlakanipha ukuze angabikhona ezitheni zenu ozalehlula loba aliphikise.
Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
16 Lizanikelwa ngabazali, ngabafowenu layizihlobo labangane njalo abanye benu bazalibulala.
Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
17 Bonke abantu bazalizonda ngenxa yami.
Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
18 Kodwa kakuyikubhubha lanwele olulodwa emakhanda enu.
Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
19 Bekezelani, lizasindiswa.
Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
20 Lingabona iJerusalema isihonqolozelwe yizimpi lizakwazi ukuthi incithakalo isisondele.
“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
21 Lapho-ke akuthi labo abaseJudiya babalekele ezintabeni, abasedolobheni kabaphume, kuthi labo abasemaphandleni bangangeni edolobheni.
A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
22 Ngoba lesi yisikhathi sokujeziswa ukugcwalisa konke okwalotshwayo.
Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
23 Yeka ubulukhuni obuzakuba khona ngalezonsuku kwabesifazane abakhulelweyo labangabadlezane! Kuzakuba khona ukuhlukuluzeka okukhulu elizweni lolaka phezu kwabantu.
Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
24 Bazakuwa ngenkemba babuthwe babe yizibotshwa zezizwe zonke. IJerusalema izagidagidwa ngabeZizwe kuze kugcwaliseke izikhathi zabeZizwe.
Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
25 Kuzabakhona izibonakaliso elangeni, enyangeni lasezinkanyezini. Emhlabeni izizwe zizakuba phakathi kosizi lokudideka ngenxa yokuhuba lokukhaphaza kolwandle.
“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
26 Abantu bazaphela amandla ngokwesaba, behlutshwa yilokho okuzayo emhlabeni, ngoba izisekelo zasezulwini zizazanyazanyiswa.
Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
27 Ngalesosikhathi bazayibona iNdodana yoMuntu isiza ngeyezi ilamandla lenkazimulo enkulu.
A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
28 Nxa lezizinto seziqala ukwenzakala manini liqine, liphakamise amakhanda enu, ngoba ukuhlengwa kwenu sekusondela.”
Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
29 Wabatshela umfanekiso lo wathi, “Khangelani esihlahleni somkhiwa kanye lezinye zonke izihlahla.
Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
30 Nxa zihluma lizazibonela lani njalo lazi ukuthi ihlobo selisondele.
A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
31 Kanjalo-ke, nxa lingabona lezizinto sezisenzakala, lazi ukuthi umbuso kaNkulunkulu ususondele.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
32 Ngilitshela iqiniso, lesisizukulwane kasiyikudlula zize zenzakale zonke lezizinto.
“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
33 Izulu lomhlaba kuzedlula, kodwa amazwi ami kawayikwedlula lanini.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
34 Nanzelelani funa inhliziyo zenu zithundubale ngokuzitika lokudakwa lokunqineka ngezinto zalimpilo, ngoba lolosuku luzalijuma njengomjibila.
“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
35 Ngoba luzafikela bonke labo abahlala kuwo wonke umhlaba.
Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
36 Hlalani lilindile, likhulekele ukuthi liphephe kukho konke osekuzakwenzeka masinyane, lokuthi libe lamandla okuma phambi kweNdodana yoMuntu.”
Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
37 Insuku zonke uJesu wayefundisa ethempelini kuthi kusihlwa aphume ayechitha ubusuku eqaqeni olwaluthiwa yiNtaba yama-Oliva,
Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
38 njalo abantu bonke babesiza ekuseni kakhulu ukuzamuzwa ethempelini.
Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.

< ULukha 21 >