< ULukha 1 >

1 Banengi asebazimisela ukuqoqa umlando wezinto esezigcwalisekile phakathi kwethu,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 njengokwedluliselwa kwazo kithi yilabo ababekhona ekuqaleni bengabafakazi lezinceku zelizwi.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Ngakho-ke, njengoba mina ngokwami sengichwayisisile konke kusukela ekuqaleni, lami ngikubone kufanele ukuthi ngikulobele umlando oqondileyo, komkhulu ohloniphekayo uTheyofelasi
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 ukuze wazi iqiniso lezinto lezo ozifundisiweyo.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Ngesikhathi sikaHerodi inkosi yaseJudiya kwakulomphristi okwakuthiwa nguZakhariya, owaye ngowesigaba sika-Abhija, umkakhe u-Elizabethi laye wayengowosendo luka-Aroni.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Bobabili babelungile emehlweni kaNkulunkulu beyilandela yonke imilayo leziqondiso zeNkosi bengasoleki.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Kodwa babengelabantwana ngoba u-Elizabethi wayeyinyumba njalo bobabili basebeluphele.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Kwenzakala ukuthi isigaba sikaZakhariya siyiso esasimiselwe umsebenzi wethempeli ngalesosikhathi,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 wadliwa yinkatho ngokomkhuba wobuphristi, ukuthi angene ethempelini leNkosi ayetshisa impepha.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Kwathi isikhathi sokutshisa impepha sesifikile, wonke amakholwa ayebuthene lapho ayekhuleka ephandle.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Kwasekubonakala kuye ingilosi yeNkosi imi ngakwesokunene kwe-alithari lempepha.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 UZakhariya wathi eyibona wethuka wesaba kakhulu.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Kodwa ingilosi yathi kuye, “Ungesabi, Zakhariya; umkhuleko wakho usuzwakele. Umkakho u-Elizabethi uzakuzalela indodana kufanele uyinike ibizo elithiwa nguJohane.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Uzakuba yintokozo lenjabulo kuwe njalo abanengi bazathokoza ngenxa yokuzalwa kwakhe,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 ngoba uzakuba mkhulu emehlweni eNkosi. Kakumelanga anathe iwayini lanini loba yini ebilisiweyo enathwayo, njalo uzagcwaliswa ngoMoya oNgcwele kusukela ekuzalweni kwakhe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Uzaletha abantu bako-Israyeli abanengi eNkosini uNkulunkulu wabo.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Uzahamba phambili kweNkosi ngomoya langamandla ka-Elija, ukuguqulela inhliziyo zaboyise ebantwaneni babo labayiziqholo elwazini lwabalungileyo, ukuqondisa abantu abalungiselelwe iNkosi.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 UZakhariya wabuza ingilosi wathi, “Ngingaba leqiniso lakho njani lokho? Sengilixhegu njalo lomkami useluphele.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Ingilosi yaphendula yathi, “NginguGabhuriyeli mina. Ngima phambi kukaNkulunkulu, ngithunywe ukuzokhuluma lawe ngikutshela ngalezi izindaba ezinhle.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Okwamanje uzakuba yisimungulu wehluleke ukukhuluma kuze kufike lolosuku okuzakwenzakala ngalo lokhu, ngoba kawuzange uwakholwe amazwi ami, wona azagcwaliseka ngesikhathi sawo esifaneleyo.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Sonke lesisikhathi abantu babelokhu bemlindele uZakhariya sebemangele ukuthi kungani wayethethe isikhathi eside kangako ethempelini.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Waphuma esesehluleka ukukhuluma labo. Babona ukuthi wayebone umbono ethempelini ngoba wayelokhu eqhweba ngezandla, kodwa esehluleka ukukhuluma.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Izopha lakhe seliphelile wabuyela ekhaya.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Ngemva kwalokhu umkakhe u-Elizabethi wazithwala wasezifihla okwezinyanga ezinhlanu,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 esithi, “INkosi ingenzele lokhu. Kulezi insuku ilutshengisile uthando Lwayo yasusa ihlazo lami ebantwini.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Ngenyanga yesithupha yokuzithwala kuka-Elizabethi, uNkulunkulu wathuma ingilosi uGabhuriyeli eNazaretha, idolobho elaliseGalile,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 ukuya entombini egcweleyo eyayithembise ukutshada lendoda eyayithiwa nguJosefa, owesizukulwane sikaDavida. Ibizo lentombi egcweleyo le kwakunguMariya.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Ingilosi yaya kuye yathi, “Sabona wena othole umusa kakhulukazi INkosi ilawe.”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Amazwi ayo amhlupha kakhulu uMariya wamangala ukuthi kanti kwakuyikubingelela bani lokhu.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Kodwa ingilosi yathi kuye, “Ungesabi Mariya, uthole umusa kuNkulunkulu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Uzakhulelwa ubelethe indodana, uyethe ibizo uthi nguJesu.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Uzaba ngumuntu omkhulu abizwe ngokuthi yiNdodana yoPhezukonke. INkosi uNkulunkulu izamupha isihlalo sikayise uDavida,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 njalo uzabusa phezu kwendlu kaJakhobe laphakade; umbuso wakhe kawuyikuphela.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 UMariya wayibuza ingilosi wathi, “Lokho kuzakwenzakala njani njengoba mina ngimsulwa ngingayazi indoda?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ingilosi yaphendula yathi, “UMoya oNgcwele uzakwehlela phezu kwakho, lamandla akhe oPhezukonke azakusibekela. Ngakho ongcwele ozazalwa uzathiwa yiNdodana kaNkulunkulu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Lo-Elizabethi isihlobo sakho uzakuba lomntwana ekuluphaleni kwakhe, yena okwakuthiwa yinyumba usesenyangeni yakhe yesithupha.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Ngoba kakukho okwehlulayo kuNkulunkulu.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 UMariya waphendula wathi, “Ngiyincekukazi yeNkosi. Kakwenzeke kimi njengoba utshilo.” Ingilosi yasisuka kuye.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Ngalesosikhathi uMariya waphanga wenza amalungiselelo waya edolobheni elizweni lamaqaqa eJudiya,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 lapho angena khona emzini kaZakhariya wabingelela u-Elizabethi.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Kwathi u-Elizabethi esizwa ukubingelela kukaMariya, umntwana weqa esiswini sakhe, u-Elizabethi wagcwala ngoMoya oNgcwele.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Wakhuluma ngelizwi eliphezulu wathi, “Ubusisiwe wena phakathi kwabesifazane, njalo ubusisiwe umntwana ozamzala!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Kodwa kungani ngithole umusa ongaka mina, ukuba ngethekelelwe ngunina weNkosi yami?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Ngonele ukuzwa ukubingelela kwakho, umntwana osesiswini sami weqa ngentokozo.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Ubusisiwe lowo osekholiwe ukuthi lokho iNkosi ethe kuzakwenzeka kuye kuzagcwaliseka!”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 UMariya wathi: “Umphefumulo wami uyayidumisa iNkosi
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 lomoya wami uyathokoza kuNkulunkulu uMsindisi wami,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 ngoba ukunanzile ukuzehlisa kwencekukazi yakhe. Kusukela manje zonke izizukulwane zizakuthi ngibusisiwe,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 ngoba uSomandla ungenzele izinto ezinkulu, lingcwele ibizo lakhe.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Isihawu sakhe sifinyelela kulabo abamesabayo, kulandela isizukulwane ngesizukulwane.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Uyenzile imisebenzi emikhulu ngengalo yakhe: ubachithizile labo abaziqakisa ngemicabango yezinhliziyo zabo.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Uwethule amakhosi ezihlalweni zawo, kodwa wabaphakamisa abantukazana.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ubasuthisile abalambileyo ngezinto ezinhle, kodwa abanothileyo ubaxotshe bengaphathanga lutho.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Uyisizile inceku yakhe u-Israyeli, wakhumbula ukuba lesihawu
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 ku-Abhrahama lezizukulwane zakhe laphakade, njengoba wakutsho kubokhokho bethu.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 UMariya wahlala lo-Elizabethi izinyanga ezazingaba ntathu wasebuyela ekhaya.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Kwathi isikhathi sika-Elizabethi sesiphelele esokubeletha wazala indodana.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Omakhelwane bakhe lezihlobo bezwa ukuthi iNkosi yayimzwele isihawu esikhulu bathokoza kanye laye.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Ngosuku lwesificaminwembili beza ukuzasoka umntwana, bafuna ukuthi bamethe ibizo likayise uZakhariya,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 kodwa unina wala wathi, “Hatshi! Kathiwe nguJohane.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Bathi kuye, “Kakho ebantwini bakini olebizo lelo.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Bakhuluma ngezandla kuyise bedinga ukuthi yena uthanda ukuthi umntwana aphiwe liphi ibizo.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Wacela isibhebhedu sokulobela, wamangalisa wonke umuntu ngoba waloba ukuthi, “Ibizo lakhe nguJohane.”
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Masinyane umlomo wakhe wavuleka lolimi lwakhe lwatshwaphuluka, waqalisa ukukhuluma edumisa uNkulunkulu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Omakhelwane bonke bamangala kakhulu, kwathi elizweni lonke lamaqaqa eJudiya abantu babekhuluma ngalezizinto.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Wonke owezwayo ngalokho wamangala ebuza esithi, “Kambe uzakuba yini umntwana lo?” Ngoba isandla seNkosi sasilaye.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Uyise uZakhariya wagcwala ngoMoya oNgcwele waphrofitha wathi:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Udumo kalube seNkosini, uNkulunkulu ka-Israyeli, ngoba ubuyile ukuzahlenga abantu bakhe.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Iluphakamisile uphondo lwensindiso yethu endlini yenceku yayo uDavida
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (njengoba yatsho ngabaphrofethi bayo abangcwele ekadeni), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 ukusindiswa ezitheni zethu lesandleni sabo bonke abasizondayo,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 ukuze atshengise isihawu kubokhokho bethu lokukhumbula isivumelwano sakhe esingcwele,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 isifungo asifunga kubaba wethu u-Abhrahama:
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 ukusikhulula esandleni sezitha zethu, size siyikhonze singelakwesaba
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 ngobungcwele langokulunga phambi kwayo ngazozonke insuku zethu.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Wena mntanami, uzathiwa ungumphrofethi woPhezukonke; ngoba uzahamba phambili kweNkosi uyilungisele indlela,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 ukunika abantu bayo ukwazi insindiso ngokuthethelelwa kwezono zabo,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 ngenxa yomusa kaNkulunkulu wethu, ilanga liphuma lize kithi livela ezulwini,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 likhanyise kulabo abahlezi ebumnyameni lasethunzini lokufa, ukukhokhelela inyawo zethu endleleni yokuthula.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Umntwana wakhula waqina emoyeni; waphila enkangala waze wavela obala ku-Israyeli.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< ULukha 1 >