< Lioka 5 >

1 Teo te nifanihisihy ama’e ondatio hijanjiñe ty tsaran’ Añahare añ’ olo’ i oñe Genesaretay
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 le nivazoho’e ty lakañe roe añ’ olon-drano ey, ie fa niakatse hanasa harato o tompo’eo.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Nijoñe an-daka’ i Simona ao re nihalaly te hisitake amy olotsey. Aa le niambesatse an-dakañe ey re nañoke ondatio.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Ie modo i fañoha’ey, le hoe re amy Simona: Mivevea mb’an-daleke mb’eo vaho ajoño ao o harato’ areoo hanarike.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Le hoe ty natoi’ i Simona aze: O Rañandria, nifanehak’ avao zahay aniankale le tsy nahazo leo raike; fe amo saontsi’oo, hajoko ao i haratoy.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Ie nanoe’ iereo zay, le nivokatse fiañe nifamorohotse nahariatañe i harato’ iareoy.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Aa le nitsikaore’e o rañe’ iareo amy lakañe ila’e eiio hañolotse iareo; nimb’eo iereo, le nipeapeà’ iareo fiañe i lakañe roe rey, vaho ho nilempotse.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Ie nahaoniñe zay t’i Simona Petera, le nihotrak’ am-pandia’ Iesoà eo nihalaly ty hoe: O Rañandria, misitaha amako fa ondaty bey hakeo.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Toe niveren-draha t’i Simona naho o rañe’eo ami’ty hamarom-piañe niazo.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Nihoe zay ka t’i Jaona naho Iakobe, ana’ i Zebedio mpitrao-pitoloñe amy Simona. Hoe t’Iesoà tamy Simona: Ko mahimahiñe fa ondaty ka ty ho tsepahe’o henane zao.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Ie toly an-tamboho ey i lakañe rey, le fonga nafoe’ iereo vaho nañorik’ aze.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Ie tan-drova raike t’Iesoà, intoy ty lahilahy atseke ty angamae; ie nahaisake Iesoà, le nihohok’ an-dahara’e nitoreo ama’e ty hoe: O Rañandria naho satri’o, mahalio ahy rehe.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Nahiti’ Iesoà ty fità’e, nitsa­pa aze le nanao ty hoe: Satriko ‘nio, maliova; naho niafak’ amy zao i haangamae’ey
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 vaho hinatahata’e tsy hitalily am’ondaty, am’ty hoe: Akia miboaha amy mpisoroñey, le ibanabanào i linili’ i Mosèy ami’ty fahaliova’o ho fitaliliañe.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Fe àntsake te niboele ty enge’e, le niropak’ ama’e i lahialeñey hijanjiñe naho ho jangañeñe amo arete’eo.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 F’ie nivike mb’ am-babangoañe añe, niloloke.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Teo te niam­besatse eo ty fariseo naho mpañoke Hake hirik’ an-drova e Galilia naho e Iehodà iaby naho boake Ierosaleme añe, le nao’e, vaho tama’e ty haozara’ i Talè hampijangañe.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Ie amy zao, nendese’ ondaty an-tihy ty lahilahy kepeke, nipay ty hanjilihañe aze ao, hampandreañe aze añatrefa’e eo.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Aa ie tsy naharendreke ty hampi­tsifirañe aze amy lahialeñey, le nanganik’ ambone’ i anjombay vaho nazotso’ iareo an-tihy, boak’an-tafo mb’ añatrefa’ Iesoà, añivo eo i mararey.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Ie nioni’e ty fatokisa’ iareo, le hoe re ama’e: O koahe, afa-tahin-drehe.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Fe nitsakore ty hoe o mpanoki-dilio naho o fariseoo: Ia o miterao? Ia ty mahafa-kakeo naho tsy i Andria­nañahare avao?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Fe nifohi’ Iesoà ty ereñeren-tro’ iareo le tinoi’e ty hoe: Ino o fitsa­korean’ arofo’ areoo?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Ty aia ty mora, ty manao ty hoe: Afa­ke o hakeo’oo? ke ty hoe: Miongaha, mañaveloa?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Aa soa te hampahafohineñe anahareo te aman-dily an-tane atoy i Ana’ ondatiy hañaha hakeo, le hoe re amy nisilofe’ i hakepehañeiy: Inao! Miongaha, tintino o tihi’oo, akia mb’ añ’ akiba’o añe.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Aa le nitroatse añatrefa’ iereo amy zao re, nandrambe i nandrea’ey vaho nimpoly, nandrenge an’ Andrianañahare.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Nilatsa iaby iereo naho nibango an’ Andrianañahare, vaho nanao ty hoe am-pañeveñañe: Nahaoniñe raha tsitantane tika anindroany.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Añe zay, le nienga t’Iesoà naho nahavazoho ty mpamory vili-loha atao Levy, niambesatse am-pandroroñañe ao, le hoe re tama’e: Oriho raho.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Aa le nifarie’e ze he’e naho niongake vaho nañorik’ aze.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Nanao sandalam-bey ho aze añ’ anjomba’e ao t’i Levy, le maro ty mpamory vili-loha naho ondaty ila’e nitrao-piambesatse am’iereo.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Fe niñeoñeoñe amo mpiama’eo o Fariseoo naho o mpanoki-dili’ iareoo ami’ty hoe: Ino ty itraofa’ areo fikama naho finoñe amo mpamory vili-lohao naho amo bey hakeoo?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Tinoi’ Iesoà ty hoe: Tsy o jangañeo ro mipay mpanaha fa o marareo;
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Tsy avy hikoike o vantañeo raho fa o mpandilatseo, hisoloho.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Le hoe ty asa’iareo tama’e: Akore te mililitse naho miloloke o mpiana’ i Jaonao, manao zay ka o amo Fariseoo, fe mitolo-pihinañe naho minoñ’ avao o Azoo?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Hoe ty natoi’ Iesoà: Lefe’ areo hao ty hampililitse ty longo’ i mpañengay ie mbe am’ iereo i mpañengay?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Mbe ho avy ty andro hanintahañe i mpañengay; hililitse amy andro zay iereo.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Hoe ka ty nirazaña’e: Tsy ia ty manakeke lamba vao ami’ty tsirodea, fa ho riate’ i vaoy naho tsy hivitrañe amy tsirodeay ty tampa’ i vaoy.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Tsy eo ka ty hañiliñe divay vao an-jonjon-kolitse hambo’e ao, kera ho tosire’ i divay vaoy i zonjon-kolitse hambo’ey vaho hianto i zonjoñey.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Tsy mete tsy ailiñ’ an-jonjoñe vao ty divay vao.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Tsy eo ty minoñe amy elay ty hipay ty vao aniany; fa hoe re: I elay ro soa.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Lioka 5 >