< Lūkas Evaņg̒elijs 8 >

1 Un pēc tam notikās, ka Viņš staigāja pa pilsētām un miestiem, mācīdams un sludinādams par Dieva valstību, un tie divpadsmit bija pie Viņa,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 Un kādas sievas, kas bija dziedinātas no ļauniem gariem un vājībām, Marija, saucama Madaļa, no kuras septiņi velni bija izgājuši,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Un Joanna, Hērodus nama uzrauga, Kūzas, sieva, un Zuzanna un daudz citas sievas, kas no sava padoma Viņam kalpoja.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Bet kad daudz ļaudis bija sanākuši un no visām pilsētām pie Viņa gāja, tad Viņš sacīja caur līdzību:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 “Sējējs izgāja, savu sēklu sēt; un sējot cita krita ceļmalā un tapa samīta, un tie putni apakš debess to apēda.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Un cita krita uz akmeni, un uzdīgusi tā sakalta, tāpēc ka tai nebija slapjuma.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Un cita krita starp ērkšķiem, un tie ērkšķi uzauga līdz un to apmāca.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Un cita krita uz labu zemi, tā uzdīga un nesa simtkārtīgus augļus.” To sacījis Viņš sauca: “Kam ausis dzirdēt, tas lai dzird.”
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Bet Viņa mācekļi Viņam vaicāja, kas šī līdzība esot?
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Bet Viņš sacīja: “Jums ir dots zināt Dieva valstības noslēpumus, bet tiem citiem caur līdzību, ka tie redzēdami neredz un dzirdēdami nesaprot.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Bet šī ir tā līdzība: tā sēkla ir Dieva vārds.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Bet kas ceļmalā, ir tie, kas to dzird; pēc velns nāk un ņem to vārdu no viņu sirdīm, lai netic un netop svēti.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Bet kas uz akmens, ir tie: kad tie to vārdu dzird, tad tie to uzņem ar prieku, bet tiem nav saknes; mazu brīdi tie tic un kārdināšanas laikā tie atkāpjās.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Bet kas starp ērkšķiem krita, ir tie, kas to dzird, bet tomēr noiet un dodas uz zūdīšanos un bagātību un pasaules kārību, un noslāpst un nenes nekādus augļus.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Bet kas labā zemē, ir tie, kas to vārdu dzird un to patur labā un godīgā sirdī, augļus nesdami iekš paciešanas.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Un sveci iededzinājis, neviens to neapklāj ar trauku nedz to liek apakš galda, bet to liek uz lukturi, lai tie, kas nāk iekšā, to gaišumu redz.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Jo nekas nav paslēpts, kas netaps redzams, nedz apslēpts, kas netaps zināms un nenāks gaismā.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Tāpēc pielūkojiet, kā jūs dzirdat! Jo kam ir, tam taps dots, un kam nav, no tā arī tas taps atņemts, ko tura par savu.”
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Bet Viņa māte un brāļi atnāca pie Viņa, un nevarēja Viņam klāt tikt to ļaužu dēļ.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Un Viņam ziņu deva un sacīja: “Tava māte un Tavi brāļi stāv ārā un grib Tevi redzēt.”
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Bet Viņš atbildēdams uz tiem sacīja: “Mana māte un Mani brāļi ir šie, kas Dieva vārdu dzird un dara.”
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Un notikās kādā dienā, ka Viņš ar Saviem mācekļiem kāpa laivā, un uz tiem sacīja: “Ejam pāri uz otru ezera malu,” un tie stūma no malas.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Un kad tie gāja ar laivu, tad Viņš aizmiga; un viesulis cēlās ezerā, un tie tapa apklāti ar viļņiem un bija lielās bēdās.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Un pie Viņa piegājuši, tie Viņu modināja sacīdami: “Kungs, Dievs, mēs grimstam!” Bet Viņš pacēlās un apdraudēja vēju un ūdens viļņus. Un tie nostājās un palika it rāmi.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Bet Viņš uz tiem sacīja: “Kur ir jūsu ticība?” Bet tie bīdamies brīnījās savā starpā sacīdami: “Kas Tas tāds, ka Viņš arī vējiem un ūdeņiem pavēl, un tie Viņam paklausa.”
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Un tie cēlās pāri uz to Gadariešu tiesu, kas ir Galilejai pretī.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Un Viņam pie malas izejot viens vīrs no tās pilsētas sastapa, kas jau ilgi bija velnu apsēsts, un neapvilka drēbes, un nestāvēja mājā, bet kapos.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Šis, Jēzu redzēdams, brēca un krita zemē Viņa priekšā un sacīja ar stipru balsi: “Kas man ar Tevi, Jēzu, Tu Dieva Tā Visuaugstākā Dēls? Es Tevi lūdzu, nemoki mani!”
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Jo Viņš tam nešķīstam garam pavēlēja, atstāties no tā cilvēka, jo tas viņu jau ilgu laiku bija plosījis, un viņš ar ķēdēm un saitēm tapa saistīts un tapa apsargāts, bet tās saites saraustījis, viņš no velna tapa dzīts uz tuksnesi.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Un Jēzus tam jautāja sacīdams: “Kā tev vārds?” Un viņš sacīja: “Leģions,” jo daudz velni iekš tā bija iegājuši
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Un tie Viņam lūdza, lai tiem nepavēlētu bezdibenī nokāpt. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Bet tur bija liels cūku pulks ganos uz kalna, un tie Viņu lūdza, ka Viņš tiem atļautu ieiet tais cūkās. Un Viņš tiem atļāva.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Un tie velni no tā cilvēka atstājušies iegāja tais cūkās, un tas pulks no kraujas nogāzās ezerā un noslīka.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Bet tie gani redzējuši, kas notika, aizbēga, un nogājuši to pasludināja pilsētā un ciemos.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Bet tie izgāja, to notikumu redzēt, un nāca pie Jēzus un atrada to cilvēku, no kā tie velni bija atstājušies, apģērbtu un prātīgu pie Jēzus kājām sēžam, un tie bijās.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Un arī tie, kas to bija redzējuši, pasludināja viņiem, kā tas velna apsēstais tapis pestīts.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Un viss tas ļaužu pulks no tās Gadariešu tiesas Viņu lūdza, ka no tiem aizietu, jo tie no lielām bailēm bija pārņemti, un Viņš kāpa laivā un griezās atpakaļ.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Bet tas vīrs, no kā tie velni bija atstājušies, Viņu ļoti lūdza, ka pie Viņa varētu palikt, bet Jēzus to atlaida sacīdams:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 “Griezies atpakaļ uz savām mājām un izteic, kādas lielas lietas Dievs tev ir darījis;” un tas nogāja pa visu to pilsētu, pasludinādams, kādas lielas lietas Jēzus tam bija darījis.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Un notikās, kad Jēzus atpakaļ nāca, tad tie ļaudis Viņu uzņēma, jo tur bija daudz, kas uz Viņu gaidīja.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Un redzi, tur nāca viens vīrs, Jaīrus vārdā, un tas bija baznīcas priekšnieks, un tas Jēzum pie kājām krizdams lūdza, ka nāktu viņa namā.
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 Jo tam bija viena vienīga meita ap divpadsmit gadiem, un tā bija nomirusi. Un Viņam ejot tie ļaudis spiedās virsū.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Un viena sieva, pie divpadsmit gadiem asins sērgā sirgusi, kas visu savu padomu bija izdevusi ārstiem un nevarējusi tapt dziedināta no neviena,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 Piegājusi no aizmugures aizskāra Viņa drēbes vīli, un tūdaļ viņas asins skriešana nostājās.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Un Jēzus sacīja: “Kas Mani aizskāris?” Un kad visi liedzās, tad Pēteris un tie, kas pie Viņa bija, sacīja: “Kungs, tie ļaudis Tev laužas virsū un Tevi spiež, un Tu saki: kas Mani aizskāris?”
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Bet Jēzus sacīja: “Mani kāds ir aizskāris; jo Es esmu manījis, ka spēks no Manis izgājis.”
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Bet tā sieva, redzēdama, ka to nevarēja slēpt, nāca drebēdama un metās ceļos priekš Viņa un Viņam izteica priekš visiem ļaudīm, kādas vainas dēļ tā Viņu bija aizskārusi, un ka tā tūdaļ bija palikusi vesela.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Bet Viņš uz to sacīja: “Turi drošu prātu, Mana meita, tava ticība tev palīdzējusi; ej ar mieru!”
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Un Viņam vēl tā runājot, viens no tā baznīcas priekšnieka saimes nāca, uz šo sacīdams: “Tava meita ir nomirusi, neapgrūtini to Mācītāju.”
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Bet Jēzus to dzirdējis tam atbildēja sacīdams: “Nebīsties, tici tikai, un viņa taps glābta.”
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Un namā iegājis, Viņš nevienu nelaida iekšā, kā vien Pēteri un Jēkabu un Jāni un tās meitas tēvu un māti.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Bet visi raudāja un to nožēloja; bet Viņš sacīja: “Neraudiet, tā nav mirusi, bet tikai guļ.”
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Un tie Viņu apsmēja, zinādami, ka tā bija nomirusi.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Bet visus izdzinis, Viņš satvēra viņas roku, sauca un sacīja: “Meitiņa, celies augšām.”
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Un viņas dvēsele atgriezās, un tā tūdaļ uzcēlās; un Viņš pavēlēja, tai dot ēst.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Un viņas vecāki iztrūcinājās. Bet Viņš tiem pavēlēja, nevienam to nesacīt, kas bija noticis.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Lūkas Evaņg̒elijs 8 >