< Lūkas Evaņg̒elijs 5 >

1 Bet notikās, kad tie ļaudis pie Viņa spiedās, Dieva vārdu dzirdēt, un Viņš stāvēja pie Ģenecaretes ezera,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Tad Viņš redzēja divas laivas pie ezera stāvam, bet tie zvejnieki bija izkāpuši un mazgāja savus tīklus.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Bet Viņš kāpa vienā laivā, kas Sīmanim piederēja, un tam lūdza, maķenīt no malas nocelt, un Viņš nosēdās un mācīja tos ļaudis no tās laivas.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Un beidzis runāt Viņš uz Sīmani sacīja: “Dodies uz augšu, un izmetiet savus tīklus, ka jūs lomu velkat.”
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Un Sīmanis atbildēja un uz Viņu sacīja: “Kungs, mēs cauru nakti strādājuši un nenieka neesam dabūjuši; bet uz Tavu vārdu es to tīklu gribu izmest.”
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Un kad tie to darīja, tad tie saņēma lielu pulku zivju, tā ka viņu tīkls saplīsa.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Un tie meta ar roku saviem biedriem, kas bija otrā laivā, lai nāktu palīgā vilkt. Un tie nāca un piepildīja abas laivas pilnas, tā ka tās tik negrima.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Kad Sīmanis Pēteris to redzēja, tad viņš krita Jēzum pie kājām un sacīja: “Kungs, izej no manis, jo es esmu grēcīgs cilvēks.”
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Jo tam izbailes bija uzgājušas un visiem, kas pie viņa bija, par šo lomu, ko tie bija vilkuši;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Tā arī Jēkabam un Jānim, Cebedeja dēliem, Sīmaņa biedriem. Un Jēzus sacīja uz Sīmani: “Nebīsties, jo no šī laika tev būs cilvēkus zvejot.”
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Un tie vilka savas laivas pie malas un, visas lietas atstājuši, gāja Viņam pakaļ.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Un notikās, kad Viņš tur bija vienā pilsētā, redzi, tad viens cilvēks, spitālības pilns, Jēzu redzēdams nometās uz savu vaigu, Viņu pielūdza un sacīja: “Kungs, ja Tu gribi, tad Tu mani vari šķīstīt.”
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Un roku izstiepis, Viņš to aizskāra sacīdams: “Es gribu, topi šķīstīts.” Un tūdaļ spitālība no tā nozuda.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Un Viņš tam pavēlēja, nevienam to nesacīt: “Bet noej un rādies priesterim un upurē par savu šķīstīšanu, ko Mozus ir pavēlējis tiem par liecību.”
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Un Viņa slava jo vairāk izpaudās, un daudz ļaudis sapulcējās, Viņu dzirdēt un tapt dziedināti no savām slimībām.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Bet Viņš nogāja tuksnesī un pielūdza Dievu.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Un notikās kādā dienā Viņam mācot, tad tur farizeji sēdēja un bauslības mācītāji, kas bija nākuši no visiem Galilejas un Jūdejas un Jeruzālemes miestiem. Un Tā Kunga spēks parādījās Viņam dziedinājot,
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Un redzi, vīri nesa uz gultas vienu cilvēku, tas bija melmeņu sērdzīgs; un tie meklēja, to ienest un nolikt Viņa priekšā.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Un neatrazdami, kur viņu ienest, to ļaužu dēļ, tie uzkāpa jumtā un to nolaida caur griestiem ar gultu pašā vidū Jēzum priekšā.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Un Tas viņu ticību redzēdams uz to sacīja: “Cilvēks, tavi grēki tev ir piedoti.”
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Un tie rakstu mācītāji un farizeji iesāka domāt pie sevis un sacīt: “Kas Tas tāds, ka Tas runā Dieva zaimošanas? Kas var grēkus piedot kā vien Tas Vienīgais Dievs?”
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Bet nomanīdams viņu domas, Jēzus atbildēja un uz tiem sacīja: “Ko jūs domājat savās sirdīs?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Kas ir vieglāki sacīt: tavi grēki tev ir piedoti, vai sacīt: celies un staigā?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Bet lai jūs zināt, ka Tam Cilvēka Dēlam ir vara virs zemes, grēkus piedot, (tad Viņš uz to melmeņu sērdzīgo sacīja: ) Es tev saku: celies un ņem savu gultu un ej uz savām mājām!”
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Un tas tūdaļ viņiem redzot pacēlās, paņēma to, uz ko tas bija gulējis, un aizgāja uz savām mājām Dievu slavēdams.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Un brīnīšanās visiem uzgāja, un tie slavēja Dievu: un tie bijāšanas pilni sacīja: “Mēs šodien brīnuma lietas esam redzējuši.”
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Un pēc tam Viņš izgāja un ieraudzīja vienu muitnieku, vārdā Levi, pie muitas sēžam un uz to sacīja: “Nāc Man pakaļ.”
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Un visu atstājis tas cēlās un gāja Viņam pakaļ.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Un Levi Viņam taisīja lielu mielastu savā namā, un tur bija liels pulks muitnieku un citu, kas līdz ar tiem apsēdās.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Un tie rakstu mācītāji un farizeji kurnēja pret Viņa mācekļiem un sacīja: “Kāpēc jūs ēdat un dzerat ar muitniekiem un grēciniekiem?”
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Un Jēzus atbildēja un uz tiem sacīja: “Veseliem ārstus nevajag, bet vājiem.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Es neesmu nācis, taisnus aicināt pie atgriešanās no grēkiem, bet grēcinekus.”
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Bet tie uz Viņu sacīja: “Kāpēc Jāņa mācekļi tik daudz gavē un Dievu lūdz, tā kā arī tie farizeju mācekļi, bet tavi ēd un dzer?”
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Bet Viņš uz tiem sacīja: “Kāzu ļaudīm jūs nevarat likt gavēt, kamēr brūtgāns pie viņiem.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Bet nāks dienas, kad brūtgāns tiem būs atņemts, tanīs dienās tad tie gavēs.”
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Un Viņš sacīja uz tiem arī līdzību: “Neviens neliek ielāpu no jaunām drēbēm uz vecām; citādi viņš tik saplēsīs tās jaunās, un tas ielāps no tām jaunām nederēs uz tām vecām.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Un neviens nelej jaunu vīnu vecos ādas traukos; citādi tas jaunais vīns tos traukus pārplēsīs un izgāzīsies, un tie trauki ies bojā;
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Bet jaunu vīnu būs liet jaunos traukos, tad abi kopā paliek veseli.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Un nevienam, kas to veco dzēris, tūdaļ neiegribās tā jaunā, jo tas saka: tas vecais ir labāks.”
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Lūkas Evaņg̒elijs 5 >