< Ecechiela 32 >

1 Un divpadsmitā gadā, divpadsmitā mēnesī pirmā mēneša dienā Tā Kunga vārds uz mani notika sacīdams:
A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Cilvēka bērns, sāc raudu dziesmu par Faraonu, Ēģiptes ķēniņu, un saki uz viņu: ak tautu lauva, tu esi pagalam! Un tu biji kā jūras zvērs jūrā un izlēci savās upēs un sajauci ūdeņus ar savām kājām un samini upes.
“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
3 Tā saka Tas Kungs Dievs: Es tādēļ Savu tīklu izplētīšu pār tevi daudz tautu sapulcē, kas tevi izvilks Manā tīklā.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
4 Tad Es tevi metīšu uz zemi, Es tevi nosviedīšu uz lauku un visiem putniem apakš debess Es likšu mist uz tevis un visiem zvēriem virs zemes no tevis pieēsties,
Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
5 Un metīšu tavu maitu uz kalniem un pildīšu tās ielejas ar tavām miesām.
Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
6 Un Es dzirdināšu zemi ar tām asinīm, kas no tevis izplūst līdz kalniem, un upes no tevis taps pildītas.
Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
7 Un kad Es tevi izdzēsīšu, tad Es apsegšu debesi un aptumšošu viņas zvaigznes, sauli Es apklāšu ar mākoņiem, un mēneša gaišums vairs nespīdēs.
Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
8 Visus spožos debess spīdekļus Es tevis dēļ aptumšošu un vedīšu tumsību pār tavu zemi, saka Tas Kungs Dievs.
Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Es arī darīšu skumīgas daudz tautu sirdis, kad Es tavu mocību iznesīšu starp tautām, tanīs valstīs, ko tu nepazīsti.
Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
10 Un Es darīšu, ka daudz tautas par tevi iztrūcinājās, un viņu ķēniņiem mati celsies stāvu par tevi, kad Es cilāšu Savu zobenu viņu priekšā, un tie drebēs ik acumirkli ikviens par savu dvēseli tai dienā, kad tu kritīsi.
Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
11 Jo tā saka Tas Kungs Dievs: Bābeles ķēniņa zobens nāks pār tevi.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
12 Un Es tavu pulku nogāzīšu caur vareno zobeniem, tie visi ir tie visbriesmīgākie starp tautām, tie izpostīs Ēģiptes lepnību, un viss viņas pulks taps izdeldēts.
Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
13 Un visus viņas lopus Es izdeldēšu pie tā lielā ūdens, ka cilvēka kāja to vairs nesajauks, ir lopu nags to nesajauks.
Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
14 Tad Es viņu ūdeņus darīšu skaidrus un viņu upēm likšu tecēt kā eļļai, saka Tas Kungs Dievs,
Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Kad Es Ēģipti būšu darījis par posta vietu, un zeme no savas pilnības būs palikusi tukša, kad Es visus viņas iedzīvotājus būšu kāvis, - tad samanīs, ka Es esmu Tas Kungs.
Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
16 Šī ir tā raudu dziesma, un tā jādzied; tautu meitas šo raudu dziesmu dziedās; par Ēģipti un par visu viņas ļaužu pulku tās dziedās šo raudu dziesmu, saka Tas Kungs Dievs. -
“Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
17 Un divpadsmitā gadā, piecpadsmitā mēneša dienā Tā Kunga vārds uz mani notika sacīdams:
A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Cilvēka bērns, žēlojies par Ēģiptes ļaužu pulku un nogremdē to līdz ar tām lepno tautu meitām zemes apakšā pie tiem, kas grimuši dziļumā.
“Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
19 Par ko tu nu esi skaistāka? Kāp zemē un apgūlies pie neapgraizītiem.
Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
20 Tie kritīs starp zobena nokautiem. Viņa ir nodota zobenam; aizraujiet viņu ar visu viņas ļaužu pulku.
Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
21 Tie varoņu varenie un viņas palīgi ar viņu runās elles vidū: tie ir nogrimuši, tie guļ starp neapgraizītiem un zobena nokautiem. (Sheol h7585)
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol h7585)
22 Tur ir Asurs ar visu savu ļaužu pulku, viņu kapi ir visapkārt ap viņu; tie visi nokauti, caur zobenu krituši.
“Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
23 Viņa kaps ir tai visdziļākā bedrē, un viņa ļaužu pulks ir visapkārt ap viņa kapu; visi nokauti, caur zobenu krituši, kas briesmas bija cēluši dzīvo zemē.
Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
24 Tur ir Elams ar visu savu ļaužu pulku visapkārt ap viņa kapu; tie visi nokauti, caur zobenu krituši; tie grimuši neapgraizīti zemes apakšā, kas briesmas bija cēluši dzīvo zemē, tie nes savu kaunu pie tiem, kas grimuši dziļumā.
“Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
25 Pie nokautiem cisas sataisītas viņam un visam viņa ļaužu pulkam, viņu kapi ir visapkārt ap viņu; tie visi, neapgraizīti, caur zobenu ir nokauti; tāpēc ka tie briesmas cēluši dzīvo zemē, tie nes savu kaunu pie tiem, kas grimuši dziļumā, - viņš guldināts nokauto vidū.
An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
26 Tur ir Mešehs un Tūbals ar visu savu ļaužu pulku, visapkārt ap viņu ir viņu kapi, tie visi, neapgraizīti, ir nokauti ar zobenu, tāpēc ka bija briesmas cēluši dzīvo zemē.
“Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
27 Tie neguļ pie tiem kritušiem neapgraizīto varoņiem, kas ellē nogrimuši ar savām bruņām, kam zobeni likti apakš galvām; viņu noziegumi nākuši pār viņu kauliem, tāpēc ka bija varoņi par briesmām dzīvo zemē. (Sheol h7585)
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol h7585)
28 Arī tu tapsi satriekts neapgraizītu vidū un gulēsi pie zobena nokautiem.
“Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
29 Tur ir Edoms, viņa ķēniņi un visi viņa lielkungi, kas ar savu varoņu godu ir likti pie zobena nokautiem; tie guļ pie neapgraizītiem un pie tiem, kas grimuši dziļumā.
“Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
30 Tur ir visi ziemeļa valdnieki un visi Sidonieši, kas nogrimuši pie nokautiem un kaunā likti, lai gan ar savu varu bijuši par iztrūcināšanu, un tie guļ neapgraizīti pie tiem, kas zobena nokauti, un nes savu kaunu pie tiem, kas nogrimuši dziļumā. -
“Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
31 Faraons tos redzēs un iepriecināsies ar visu savu ļaužu pulku; ar zobenu ir nokauti, Faraons un viss viņa karaspēks, saka Tas Kungs Dievs.
“Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
32 Jo Es viņam esmu licis briesmas celt dzīvo zemē, un viņš ir nolikts neapgraizīto vidū pie tiem, kas zobena nokauti, Faraons ar visu savu ļaužu pulku, saka Tas Kungs Dievs.
Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ecechiela 32 >