< Otra Samuela 11 >

1 Un kad gads bija pagājis, ap to laiku, kad ķēniņi mēdz iziet, tad Dāvids sūtīja Joabu un savus kalpus viņam līdz un visu Israēli, un tie postīja Amona bērnus un apmetās pret Rabu; bet Dāvids palika Jeruzālemē.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Un notikās ap vakara laiku, ka Dāvids cēlās no savas gultas un staigāja pa ķēniņa nama jumtu un redzēja no jumta sievu mazgājamies, un šī sieva bija ļoti skaista no skata.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 Un Dāvids nosūtīja un lika vaicāt pēc tās sievas; tad sacīja: tā ir Batseba, Elijama meita, Hetieša Ūrijas sieva.
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 Tad Dāvids sūtīja vēstnešus un to lika atvest, un tā nāca pie viņa un viņš pie tās gulēja, un kad viņa no savas nešķīstības bija šķīstījusies, tad viņa atkal gāja mājās.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 Un tā sieva tapa grūta. Tad viņa nosūtīja un deva Dāvidam ziņu un sacīja: es esmu grūta.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Tad Dāvids sūtīja pie Joaba sacīdams: sūti to Etieti Ūriju pie manis. Un Joabs sūtīja Ūriju pie Dāvida.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Kad nu Ūrija pie viņa atnāca, tad Dāvids vaicāja: kā iet Joabam, kā iet ļaudīm un kā iet karā.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Un Dāvids sacīja uz Ūriju: noej savā namā un mazgā savas kājas. Un kad Ūrija no ķēniņa nama izgāja, tad viņam ķēniņa dāvanas tapa nestas pakaļ.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Bet Ūrija apgūlās priekš ķēniņa nama durvīm ar visiem sava kunga kalpiem un negāja mājās.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Un Dāvidam deva ziņu un sacīja: Ūrija nav gājis uz mājām. Tad Dāvids sacīja uz Ūriju: Vai tu nenāci no ceļa? Kāpēc tu nenoej savā namā?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Un Ūrija sacīja uz Dāvidu: Dieva šķirsts un Israēls un Jūda paliek teltīs, un mans kungs Joabs un mana kunga kalpi mīt laukā; vai tad es ietu mājās ēst un dzert un pie savas sievas gulēt? Tik tiešām kā tu dzīvs un tava dvēsele dzīva, es to nedarīšu.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Tad Dāvids sacīja uz Ūriju: paliec arī šodien šeitan, tad es tev rītu atlaidīšu. Tā Ūrija palika Jeruzālemē šo un otru dienu.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Un Dāvids to aicināja, ka tas viņa priekšā ēda un dzēra, un viņš to piedzirdināja. Un vakarā viņš izgāja apgulties savās cisās ar sava kunga kalpiem, un viņš nenogāja mājās.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Un otrā rītā Dāvids rakstīja grāmatu Joabam un to sūtīja caur Ūriju.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Un tai grāmatā viņš tā bija rakstījis: nostādiet Ūriju tai vietā, kur tā visgrūtākā kaušanās, un novēršaties aiz viņa, ka viņš top kauts un mirst.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Un notikās, kad Joabs to pilsētu aplenca, tad viņš nostādīja Ūriju tādā vietā, kur viņš zināja, ka tur bija stipri vīri.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Kad nu pilsētas vīri izgāja un ar Joabu kāvās, tad krita kādi no tiem ļaudīm, no Dāvida kalpiem, un Etietis Ūrija arī nomira.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Tad Joabs sūtīja un deva Dāvidam ziņu par visām karalietām.
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 Un viņš pavēlēja tam vēstnesim un sacīja: kad tu būsi ķēniņam izstāstījis visas karalietas,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 Un ķēniņam dusmas celsies un viņš uz tevi sacīs: kāpēc jūs tik tuvu pie pilsētas esat gājuši kauties? Vai jūs nezinājāt, ka no mūra šaus?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Kas Abimeleku, JerubBezeta dēlu, ir nokāvis? Vai sieva uz viņu nemeta dzirnu akmeni no mūra, ka tas Tebecā nomira? Kāpēc esat gājuši tik tuvu pie mūra? Tad saki: tavs kalps Ūrija, tas Etietis, arīdzan nomiris.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Un tas vēstnesis nogāja un nāca un stāstīja Dāvidam visu, par ko Joabs viņu bija sūtījis.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Un tas vēstnesis sacīja uz Dāvidu: tie vīri bija stiprāki nekā mēs, un iznāca pret mums laukā, bet mēs viņiem pretī turējāmies līdz pat vārtu durvīm.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Tad strēlnieki no mūra šāva uz taviem kalpiem, ka kādi no ķēniņa kalpiem nomira,
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Un tavs kalps Ūrija, tas Etietis, arīdzan nomiris. Tad Dāvids sacīja uz to vēstnesi: Tā saki uz Joabu: lai tev sirds neēdās šīs lietas dēļ, jo zobens rij te šo, te citu, stāvi jo stipri karā pret to pilsētu un izposti to, - un tā iedrošini viņu.
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Kad nu Ūrijas sieva dzirdēja, ka viņas vīrs Ūrija bija miris, tad viņa gaudās par savu kungu.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Un kad gaudu laiks bija pagājis, tad Dāvids nosūtīja un to ņēma savā namā, un tā viņam palika par sievu un viņam dzemdēja dēlu. Bet šī lieta, ko Dāvids darīja, Tam Kungam nepatika.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< Otra Samuela 11 >