< Psalmorum 96 >

1 quando domus aedificabatur post captivitatem canticum huic David cantate Domino canticum novum cantate Domino omnis terra
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 cantate Domino benedicite nomini eius adnuntiate diem de die salutare eius
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 adnuntiate inter gentes gloriam eius in omnibus populis mirabilia eius
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 quoniam magnus Dominus et laudabilis valde terribilis est super omnes deos
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 quoniam omnes dii gentium daemonia at vero Dominus caelos fecit
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 confessio et pulchritudo in conspectu eius sanctimonia et magnificentia in sanctificatione eius
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 adferte Domino patriae gentium adferte Domino gloriam et honorem
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 adferte Domino gloriam nomini eius tollite hostias et introite in atria eius
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 adorate Dominum in atrio sancto eius commoveatur a facie eius universa terra
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 dicite in gentibus quia Dominus regnavit etenim correxit orbem qui non movebitur iudicabit populos in aequitate
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 laetentur caeli et exultet terra commoveatur mare et plenitudo eius
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 gaudebunt campi et omnia quae in eis sunt tunc exultabunt omnia ligna silvarum
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 a facie Domini quia venit quoniam venit iudicare terram iudicabit orbem terrae in aequitate et populos in veritate sua
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.

< Psalmorum 96 >