< Psalmorum 94 >

1 psalmus David quarta sabbati Deus ultionum Dominus Deus ultionum libere egit
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 exaltare qui iudicas terram redde retributionem superbis
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 usquequo peccatores Domine usquequo peccatores gloriabuntur
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 effabuntur et loquentur iniquitatem loquentur omnes qui operantur iniustitiam
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 populum tuum Domine humiliaverunt et hereditatem tuam vexaverunt
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 viduam et advenam interfecerunt et pupillos occiderunt
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 et dixerunt non videbit Dominus nec intelleget Deus Iacob
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 intellegite qui insipientes estis in populo et stulti aliquando sapite
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 qui plantavit aurem non audiet aut qui finxit oculum non considerat
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 qui corripit gentes non arguet qui docet hominem scientiam
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 Dominus scit cogitationes hominum quoniam vanae sunt
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 beatus homo quem tu erudieris Domine et de lege tua docueris eum
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 ut mitiges ei a diebus malis donec fodiatur peccatori fovea
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 quia non repellet Dominus plebem suam et hereditatem suam non derelinquet
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 quoadusque iustitia convertatur in iudicium et qui iuxta illam omnes qui recto sunt corde diapsalma
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 quis consurget mihi adversus malignantes aut quis stabit mecum adversus operantes iniquitatem
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 nisi quia Dominus adiuvit me paulo minus habitavit in inferno anima mea (questioned)
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 si dicebam motus est pes meus misericordia tua Domine adiuvabat me
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 secundum multitudinem dolorum meorum in corde meo consolationes tuae laetificaverunt animam meam
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 numquid aderit tibi sedis iniquitatis qui fingis dolorem in praecepto
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 captabunt in animam iusti et sanguinem innocentem condemnabunt
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 et factus est Dominus mihi in refugium et Deus meus in adiutorem spei meae
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 et reddet illis iniquitatem ipsorum et in malitia eorum disperdet eos disperdet illos Dominus Deus noster
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Psalmorum 94 >