< Psalmorum 44 >

1 in finem filiis Core ad intellectum
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Deus auribus nostris audivimus patres nostri adnuntiaverunt nobis opus quod operatus es in diebus eorum in diebus antiquis
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 manus tua gentes disperdit et plantasti eos adflixisti populos et expulisti eos
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 nec enim in gladio suo possederunt terram et brachium eorum non salvavit eos sed dextera tua et brachium tuum et inluminatio faciei tuae quoniam conplacuisti in eis
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 tu es ipse rex meus et Deus meus qui mandas salutes Iacob
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 in te inimicos nostros ventilabimus cornu et in nomine tuo spernemus insurgentes in nobis
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 non enim in arcu meo sperabo et gladius meus non salvabit me
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 salvasti enim nos de adfligentibus nos et odientes nos confudisti
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 in Deo laudabimur tota die et in nomine tuo confitebimur in saeculum diapsalma
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 nunc autem reppulisti et confudisti nos et non egredieris in virtutibus nostris
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 avertisti nos retrorsum post inimicos nostros et qui oderunt nos diripiebant sibi
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 dedisti nos tamquam oves escarum et in gentibus dispersisti nos
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 vendidisti populum tuum sine pretio et non fuit multitudo in commutationibus nostris
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 posuisti nos obprobrium vicinis nostris subsannationem et derisum his qui in circuitu nostro
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 posuisti nos in similitudinem gentibus commotionem capitis in populis
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 tota die verecundia mea contra me est et confusio faciei meae cooperuit me
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 a voce exprobrantis et obloquentis a facie inimici et persequentis
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 haec omnia venerunt super nos nec obliti sumus te et inique non egimus in testamento tuo
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 et non recessit retrorsum cor nostrum et declinasti semitas nostras a via tua
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 quoniam humiliasti nos in loco adflictionis et cooperuit nos umbra mortis
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 si obliti sumus nomen Dei nostri et si expandimus manus nostras ad deum alienum
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 nonne Deus requiret ista ipse enim novit abscondita cordis quoniam propter te mortificamur omni die aestimati sumus sicut oves occisionis
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 exsurge quare dormis Domine exsurge et ne repellas in finem
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 quare faciem tuam avertis oblivisceris inopiae nostrae et tribulationis nostrae
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 quoniam humiliata est in pulvere anima nostra conglutinatus est in terra venter noster
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 exsurge adiuva nos et redime nos propter nomen tuum
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psalmorum 44 >