< Psalmorum 37 >

1 ipsi David noli aemulari in malignantibus neque zelaveris facientes iniquitatem
Ta Dawuda. Kada ka tsorata saboda mugayen mutane ko ka yi kishin waɗanda suka aikata mugunta;
2 quoniam tamquam faenum velociter arescent et quemadmodum holera herbarum cito decident
gama kamar ciyawa za su bushe, kamar ɗanyun ganyaye za su mutu.
3 spera in Domino et fac bonitatem et inhabita terram et pasceris in divitiis eius
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
4 delectare in Domino et dabit tibi petitiones cordis tui
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
5 revela Domino viam tuam et spera in eum et ipse faciet
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
6 et educet quasi lumen iustitiam tuam et iudicium tuum tamquam meridiem
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
7 subditus esto Domino et ora eum noli aemulari in eo qui prosperatur in via sua in homine faciente iniustitias
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
8 desine ab ira et derelinque furorem noli aemulari ut maligneris
Kada ka yi fushi kada kuma ka yi hasala; kada ka tsorata, wannan yakan kai ga mugunta ne kawai.
9 quoniam qui malignantur exterminabuntur sustinentes autem Dominum ipsi hereditabunt terram
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
10 et adhuc pusillum et non erit peccator et quaeres locum eius et non invenies
A ɗan ƙanƙanen lokaci, mugaye za su shuɗe; ko ka neme su, ba za a same su ba.
11 mansueti autem hereditabunt terram et delectabuntur in multitudine pacis
Amma masu tawali’u za su gāji ƙasar su kuma zauna da cikakkiyar salama.
12 observabit peccator iustum et stridebit super eum dentibus suis
Mugaye sukan shirya wa adalai maƙarƙashiya su ciji baki a kansu;
13 Dominus autem inridebit eum quia prospicit quoniam veniet dies eius
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
14 gladium evaginaverunt peccatores intenderunt arcum suum ut decipiant pauperem et inopem ut trucident rectos corde
Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
15 gladius eorum intret in corda ipsorum et arcus ipsorum confringatur
Amma takubansu za su soki zukatansu, kuma bakkunansu za su kakkarye.
16 melius est modicum iusto super divitias peccatorum multas
Ƙanƙanen abin da mai adalci yake da shi ya fi arzikin mugaye yawa;
17 quoniam brachia peccatorum conterentur confirmat autem iustos Dominus
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
18 novit Dominus dies inmaculatorum et hereditas eorum in aeternum erit
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
19 non confundentur in tempore malo et in diebus famis saturabuntur
A lokutan masifu ba za su yanƙwane ba; a kwanakin yunwa za su sami a yalwace.
20 quia peccatores peribunt inimici vero Domini mox honorificati fuerint et exaltati deficientes quemadmodum fumus defecerunt
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
21 mutuabitur peccator et non solvet iustus autem miseretur et tribuet
Mugaye kan yi rance ba sa kuma biya, amma masu adalci suna bayar hannu sake;
22 quia benedicentes ei hereditabunt terram maledicentes autem ei disperibunt
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
23 apud Dominum gressus hominis dirigentur et viam eius volet
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
24 cum ceciderit non conlidetur quia Dominus subponit manum suam
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
25 iunior fui et senui et non vidi iustum derelictum nec semen eius quaerens panes
Dā ni yaro ne amma yanzu na tsufa, duk da haka ban taɓa ganin an yashe masu adalci ba ko a ce’ya’yansu suna roƙon burodi.
26 tota die miseretur et commodat et semen illius in benedictione erit
Kullum suna bayar hannu sake suna kuma ba da bashi ba da wahala ba, za a yi wa’ya’yansu albarka.
27 declina a malo et fac bonum et inhabita in saeculum saeculi
Ku juyo daga mugunta ku yi alheri; sa’an nan za ku zauna a ƙasar har abada.
28 quia Dominus amat iudicium et non derelinquet sanctos suos in aeternum conservabuntur iniusti punientur et semen impiorum peribit
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya,’ya’yan mugaye za su hallaka.
29 iusti autem hereditabunt terram et inhabitabunt in saeculum saeculi super eam
Masu adalci za su gāji ƙasar su kuma zauna a cikinta har abada.
30 os iusti meditabitur sapientiam et lingua eius loquetur iudicium
Bakin mutum mai adalci yakan yi magana da hikima, harshensa kuwa yakan yi maganar abin da yake daidai.
31 lex Dei eius in corde ipsius et non subplantabuntur gressus eius
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
32 considerat peccator iustum et quaerit mortificare eum
Mugaye suna fako suna jira masu adalci, suna ƙoƙari neman ransu;
33 Dominus autem non derelinquet eum in manus eius nec damnabit eum cum iudicabitur illi
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
34 expecta Dominum et custodi viam eius et exaltabit te ut hereditate capias terram cum perierint peccatores videbis
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
35 vidi impium superexaltatum et elevatum sicut cedros Libani
Na ga wani mugu, azzalumi, yana yaɗuwa kamar ɗanyen itace a asalin ƙasarsa,
36 et transivi et ecce non erat et quaesivi eum et non est inventus locus eius
amma yakan mutu nan da nan kuma ba ya ƙara kasancewa; ko an neme shi, ba za a same shi ba.
37 custodi innocentiam et vide aequitatem quoniam sunt reliquiae homini pacifico
Ka dubi marasa zargi, ka lura da adali; akwai sa zuciya domin mutum mai salama.
38 iniusti autem disperibunt simul reliquiae impiorum peribunt
Amma za a hallaka dukan masu zunubi; za a yanke sa zuciya ta mugaye.
39 salus autem iustorum a Domino et protector eorum in tempore tribulationis
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
40 et adiuvabit eos Dominus et liberabit eos et eruet eos a peccatoribus et salvabit eos quia speraverunt in eo
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.

< Psalmorum 37 >