< Psalmorum 3 >

1 psalmus David cum fugeret a facie Abessalon filii sui Domine quid multiplicati sunt qui tribulant me multi insurgunt adversum me
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
2 multi dicunt animae meae non est salus ipsi in Deo eius diapsalma
Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
3 tu autem Domine susceptor meus es gloria mea et exaltans caput meum
Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
4 voce mea ad Dominum clamavi et exaudivit me de monte sancto suo diapsalma
Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
5 ego dormivi et soporatus sum exsurrexi quia Dominus suscipiet me
Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
6 non timebo milia populi circumdantis me exsurge Domine salvum me fac Deus meus
Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
7 quoniam tu percussisti omnes adversantes mihi sine causa dentes peccatorum contrivisti
Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
8 Domini est salus et super populum tuum benedictio tua
Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)

< Psalmorum 3 >