< Psalmorum 17 >

1 oratio David exaudi Domine iustitiam meam intende deprecationem meam auribus percipe orationem meam non in labiis dolosis
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 de vultu tuo iudicium meum prodeat oculi tui videant aequitates
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 probasti cor meum visitasti nocte igne me examinasti et non est inventa in me iniquitas
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 ut non loquatur os meum opera hominum propter verba labiorum tuorum ego custodivi vias duras
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 perfice gressus meos in semitis tuis ut non moveantur vestigia mea
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 ego clamavi quoniam exaudisti me Deus inclina aurem tuam mihi et exaudi verba mea
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 mirifica misericordias tuas qui salvos facis sperantes in te
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 a resistentibus dexterae tuae custodi me ut pupillam oculi sub umbra alarum tuarum proteges me
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 a facie impiorum qui me adflixerunt inimici mei animam meam circumdederunt super me;
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 adipem suum concluserunt os eorum locutum est superbia
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 proicientes me nunc circumdederunt me oculos suos statuerunt declinare in terram
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 susceperunt me sicut leo paratus ad praedam et sicut catulus leonis habitans in abditis
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 exsurge Domine praeveni eum et subplanta eum eripe animam meam ab impio frameam tuam
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 ab inimicis manus tuae Domine a paucis de terra divide eos in vita eorum de absconditis tuis adimpletus est venter eorum saturati sunt filiis et dimiserunt reliquias suas parvulis suis
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 ego autem in iustitia apparebo conspectui tuo satiabor cum apparuerit gloria tua
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalmorum 17 >