< Psalmorum 115 >

1 non nobis Domine non nobis sed nomini tuo da gloriam
Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
2 super misericordia tua et veritate tua nequando dicant gentes ubi est Deus eorum
Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
3 Deus autem noster in caelo omnia quaecumque voluit fecit
Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
4 simulacra gentium argentum et aurum opera manuum hominum
Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
5 os habent et non loquentur oculos habent et non videbunt
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
6 aures habent et non audient nares habent et non odorabuntur
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
7 manus habent et non palpabunt pedes habent et non ambulabunt non clamabunt in gutture suo
suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
8 similes illis fiant qui faciunt ea et omnes qui confidunt in eis
Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
9 domus Israhel speravit in Domino adiutor eorum et protector eorum est
Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
10 domus Aaron speravit in Domino adiutor eorum et protector eorum est
Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
11 qui timent Dominum speraverunt in Domino adiutor eorum et protector eorum est
Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
12 Dominus memor fuit nostri et benedixit nobis benedixit domui Israhel benedixit domui Aaron
Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
13 benedixit omnibus qui timent Dominum pusillis cum maioribus
zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
14 adiciat Dominus super vos super vos et super filios vestros
Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
15 benedicti vos Domino qui fecit caelum et terram
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
16 caelum caeli Domino terram autem dedit filiis hominum
Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
17 non mortui laudabunt te Domine neque omnes qui descendunt in infernum (questioned)
Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
18 sed nos qui vivimus benedicimus Domino ex hoc nunc et usque in saeculum
mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.

< Psalmorum 115 >