< Job 28 >

1 habet argentum venarum suarum principia et auro locus est in quo conflatur
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 ferrum de terra tollitur et lapis solutus calore in aes vertitur
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 tempus posuit tenebris et universorum finem ipse considerat lapidem quoque caliginis et umbram mortis
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 dividit torrens a populo peregrinante eos quos oblitus est pes egentis hominum et invios
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 terra de qua oriebatur panis in loco suo igne subversa est
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 locus sapphyri lapides eius et glebae illius aurum
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 semitam ignoravit avis nec intuitus est oculus vulturis
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 non calcaverunt eam filii institorum nec pertransivit per eam leaena
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 ad silicem extendit manum suam subvertit a radicibus montes
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 in petris rivos excidit et omne pretiosum vidit oculus eius
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 profunda quoque fluviorum scrutatus est et abscondita produxit in lucem
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 sapientia vero ubi invenitur et quis est locus intellegentiae
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 nescit homo pretium eius nec invenitur in terra suaviter viventium
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 abyssus dicit non est in me et mare loquitur non est mecum
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 non dabitur aurum obrizum pro ea nec adpendetur argentum in commutatione eius
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 non conferetur tinctis Indiae coloribus nec lapidi sardonico pretiosissimo vel sapphyro
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 non adaequabitur ei aurum vel vitrum nec commutabuntur pro ea vasa auri
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 excelsa et eminentia non memorabuntur conparatione eius trahitur autem sapientia de occultis
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 non adaequabitur ei topazium de Aethiopia nec tincturae mundissimae conponetur
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 unde ergo sapientia veniet et quis est locus intellegentiae
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 abscondita est ab oculis omnium viventium volucres quoque caeli latet
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 perditio et mors dixerunt auribus nostris audivimus famam eius
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 Deus intellegit viam eius et ipse novit locum illius
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 ipse enim fines mundi intuetur et omnia quae sub caelo sunt respicit
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 qui fecit ventis pondus et aquas adpendit mensura
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 quando ponebat pluviis legem et viam procellis sonantibus
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 tunc vidit illam et enarravit et praeparavit et investigavit
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 et dixit homini ecce timor Domini ipsa est sapientia et recedere a malo intellegentia
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”

< Job 28 >