< Marcum 3 >

1 Et introivit iterum in synagogam: et erat ibi homo habens manum aridam.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 Et observabant eum, si sabbatis curaret, ut accusarent illum.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 Et ait homini habenti manum aridam: Surge in medium.
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 Et dicit eis: Licet sabbatis benefacere, an male? animam salvam facere, an perdere? At illi tacebant.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 Et circumspiciens eos cum ira, contristatus super caecitate cordis eorum, dicit homini: Extende manum tuam. Et extendit, et restituta est manus illi.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 Exeuntes autem Pharisaei, statim cum Herodianis consilium faciebant adversus eum quomodo eum perderent.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Iesus autem cum discipulis suis secessit ad mare: et multa turba a Galilaea, et Iudaea secuta est eum,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 et ab Ierosolymis, et ab Idumaea, et trans Iordanem: et qui circa Tyrum, et Sidonem, multitudo magna, audientes, quae faciebat, venerunt ad eum.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 Et dixit Iesus discipulis suis ut in navicula sibi deservirent propter turbam, ne comprimerent eum.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 multos enim sanabat ita ut irruerent in eum ut illum tangerent quotquot habebant plagas.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 Et spiritus immundi, cum illum videbant, procidebant ei: et clamabant dicentes:
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 Tu es Filius Dei. Et vehementer comminabatur eis ne manifestarent illum.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 Et ascendens in montem vocavit ad se quos voluit ipse: et venerunt ad eum.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 Et fecit ut essent duodecim cum illo: et ut mitteret eos praedicare.
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 Et dedit illis potestatem curandi infirmitates, et eiiciendi daemonia.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 Et imposuit Simoni nomen Petrus:
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 et Iacobum Zebedaei, et Ioannem fratrem Iacobi, et imposuit eis nomina Boanerges, quod est, Filii tonitrui:
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 et Andraeam, et Philippum, et Bartholomaeum, et Matthaeum, et Thomam, et Iacobum Alphaei, et Thaddaeum, et Simonem Cananaeum,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 et Iudam Iscariotem, qui et tradidit illum.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Et veniunt ad domum: et convenit iterum turba, ita ut non possent neque panem manducare.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 Et cum audissent sui, exierunt tenere eum: dicebant enim: Quoniam in furorem versus est.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 Et Scribae, qui ab Ierosolymis descenderant, dicebant: Quoniam Beelzebub habet, et quia in principe daemoniorum eiicit daemonia.
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 Et convocatis eis in parabolis dicebat illis: Quomodo potest satanas satanam eiicere?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 Et si regnum in se dividatur, non potest regnum illud stare.
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 Et si domus super semetipsam dispertiatur, non potest domus illa stare.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 Et si satanas consurrexerit in semetipsum, dispertitus est, et non poterit stare, sed finem habet.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Nemo potest vasa fortis ingressus in domum diripere, nisi prius fortem alliget, et tunc domum eius diripiet.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 Amen dico vobis, quoniam omnia dimittentur filiis hominum peccata, et blasphemiae, quibus blasphemaverint:
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 qui autem blasphemaverit in Spiritum sanctum, non habebit remissionem in aeternum, sed reus erit aeterni delicti. (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Quoniam dicebant: Spiritum immundum habet.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 Et veniunt mater eius et fratres: et foris stantes miserunt ad eum vocantes eum,
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 et sedebat circa eum turba: et dicunt ei: Ecce mater tua, et fratres tui foris quaerunt te.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 Et respondens eis, ait: Quae est mater mea, et fratres mei?
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Et circumspiciens eos, qui in circuitu eius sedebant, ait: Ecce mater mea, et fratres mei.
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Qui enim fecerit voluntatem Dei, hic frater meus, et soror mea, et mater est.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Marcum 3 >