< Psalmorum 22 >

1 In finem pro susceptione matutina, Psalmus David. Deus Deus meus respice in me: quare me dereliquisti? longe a salute mea verba delictorum meorum.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Deus meus clamabo per diem, et non exaudies: et nocte, et non ad insipientiam mihi.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Tu autem in sancto habitas, Laus Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 In te speraverunt patres nostri: speraverunt, et liberasti eos.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Ad te clamaverunt, et salvi facti sunt: in te speraverunt, et non sunt confusi.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Ego autem sum vermis, et non homo: opprobrium hominum, et abiectio plebis.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Omnes videntes me, deriserunt me: locuti sunt labiis, et moverunt caput.
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 Speravit in Domino, eripiat eum: salvum faciat eum, quoniam vult eum.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Quoniam tu es, qui extraxisti me de ventre: spes mea ab uberibus matris meæ.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 In te proiectus sum ex utero: de ventre matris meæ Deus meus es tu,
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 ne discesseris a me: Quoniam tribulatio proxima est: quoniam non est qui adiuvet.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Circumdederunt me vituli multi: tauri pingues obsederunt me.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Aperuerunt super me os suum, sicut leo rapiens et rugiens.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Sicut aqua effusus sum: et dispersa sunt omnia ossa mea. Factum est cor meum tamquam cera liquescens in medio ventris mei.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Aruit tamquam testa virtus mea, et lingua mea adhæsit faucibus meis: et in pulverem mortis deduxisti me.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Quoniam circumdederunt me canes multi: concilium malignantium obsedit me. Foderunt manus meas et pedes meos:
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 dinumeraverunt omnia ossa mea. Ipsi vero consideraverunt et inspexerunt me:
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 diviserunt sibi vestimenta mea, et super vestem meam miserunt sortem.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Tu autem Domine ne elongaveris auxilium tuum a me: ad defensionem meam conspice.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Erue a framea Deus animam meam: et de manu canis unicam meam:
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Salva me ex ore leonis: et a cornibus unicornium humilitatem meam.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Narrabo nomen tuum fratribus meis: in medio ecclesiæ laudabo te.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Qui timetis Dominum laudate eum: universum semen Iacob glorificate eum:
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Timeat eum omne semen Israel: quoniam non sprevit, neque despexit deprecationem pauperis: Nec avertit faciem suam a me: et cum clamarem ad eum exaudivit me.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 Apud te laus mea in ecclesia magna: vota mea reddam in conspectu timentium eum.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Edent pauperes, et saturabuntur: et laudabunt Dominum qui requirunt eum: vivent corda eorum in sæculum sæculi.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Reminiscentur et convertentur ad Dominum universi fines terræ: Et adorabunt in conspectu eius universæ familiæ Gentium.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Quoniam Domini est regnum: et ipse dominabitur Gentium.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Manducaverunt et adoraverunt omnes pingues terræ: in conspectu eius cadent omnes qui descendunt in terram.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Et anima mea illi vivet: et semen meum serviet ipsi.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Annunciabitur Domino generatio ventura: et annunciabunt cæli iustitiam eius populo qui nascetur, quem fecit Dominus.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psalmorum 22 >