< Luke 8 >

1 Kutu pacl tok Jesus el fufahsryesr in siti srisrik ac siti lulap in fahkak Pweng Wo ke Tokosrai lun God. Mwet singoul luo ah welul,
Bayan haka, Yesu da almajiransa goma sha biyu, su ka zagaya cikin birane da kauyuka dabam dabam, suna wa'azi da shelar labari mai dadi game da mulkin Allah,
2 ac oayapa kutu mutan ma el tuh akkeyala liki kain in mas ac ngun fohkfok ma oan yorolos elos welul pac: Mary (su pangpang Magdalene), su ngun fohkfok itkosr lisyukla lukel;
mata da yawa wadanda Yesu ya warkar daga aljanu da cututtuka iri iri suna tafiya tare da su. A cikinsu akwai Maryamu wadda a ke ce da ita Magadaliya, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta,
3 Joanna, mutan kial Chuza, mwet kulansap fulat inkul sel Herod; ac Susanna — wi mutan pus pac saya su sang ma lalos sifacna in kasrel Jesus ac mwet tumal lutlut.
da Yuwana matar Kuza wakilin Hirudus, da Suzanatu da kuma wasu mata da yawa. Daga abin hannunsu suka tanada masu.
4 Mwet uh nuna fahsrna nu yurin Jesus liki acn nukewa; ac ke sie u na lulap fahsreni, Jesus el fahk pupulyuk se inge:
Wata rana aka tara taron mutane da yawa, saboda mutane su na zuwa daga birane da yawa domin su ga Yesu. Ya yi magana dasu cikin misali.
5 “Mwet se som in taknelik wheat. Ke el sisalik fita uh nu infohk uh, kutu fita uh putati nu sisken inkanek uh, yen mwet uh longya, ac won uh kangla.
“Wani mai shuka ya tafi domin ya shuka iri. Sa'adda ya ke yafa iri, wadansu iri suka fada a kan hanya. Sai mutane suka tattake su, tsuntsaye kuma suka tsince wadansu suka cinye.
6 Kutu putati nu in acn eoteot, ac ke srunak, sa na masla mweyen wangin kof ke fohk uh.
Wadansu kuma suka fada a kan duwatsu inda babu kasa da yawa. Da suka tsaro suka fara girma, sai nan da nan suka bushe saboda babu laima a wurin.
7 Kutu sin fita uh putati nu in acn ma oasr okan kokul we, wi na sacn uh kapak ac kupoiya.
Wadansu irin kuma suka fada inda yake da kayayuwa. Tsiretsiren kayayuwan suka fito tare da irin da aka shuka, suka shake su yadda basu iya yin girma ba.
8 Ac kutu putati nu in fohk wo — ma inge kapak ac oswe fahko wo, kais siofok ke ma soko.” Na Jesus el fahk ke pusra lulap, “Kowos in lohng ma inge fin oasr srewos!”
Amma wadansu irin suka fada a kan kasa mai kyau, suka yi girma sosai suka ba da anfani da yawa, har rubi dari.” Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi kira gare su, “Duk mai kunnen ji, bari ya ji.”
9 Mwet tumal lutlut elos siyuk sin Jesus lah mea kalmen pupulyuk sac,
Sai almajiran Yesu suka tambaye shi ya gaya ma su ma'anar labarin.
10 ac el topuk ac fahk, “Etauk ke ma lukma ke Tokosrai lun God uh itukot tari nu suwos, tusruktu nu sin mwet saya uh ma inge tuku in luman pupulyuk, elos in mau suk a tia liyauk, ac elos in lohng a tia kalem kac.”
ya ce da su, “Ku aka ba dama ku gane boyayyun abubuwa, na mulkin Allah. Amma ga sauran mutane ina yi masu magana cikin misalai, 'Domin ko da sun gani ba za su gane ba, kuma ko da sun ji ba za su fahimta ba.”
11 “Pa inge kalmen pupulyuk sac: Fita inge pa kas lun God.
To ga ma'anar misalin. Irin shi ne maganar Allah.
12 Fita ma putati sisken inkanek uh pa mwet su lohng kas lun God, na Devil el tuku ac eisla kas inge liki insialos elos in mau tia lulalfongi ac moulla kac.
Irin da ya fada a kan hanya sune mutanen da suka ji maganar Allah amma daga baya sai shedan ya zo ya dauke maganar daga cikin hankulansu, domin kada su bada gaskiya su tsira.
13 Fita ma putati nu in fohk eoteot uh pa mwet su lohng kas inge ac insewowo kac. Tusruktu kas uh tiana putati loal in elos. Elos lulalfongi na ke kitin pacl, a ke mwe sruhf uh sonolos, na elos ikori.
Sa'annan, wadanda suka fada kan duwatsu sune mutanen da, da zarar sun ji maganar, sukan karbe ta da murna, amma ba su da sauyu; su kan bada gaskiya na dan lokaci kadan kawai, da zaran gwaji ya same su sai su ridda.
14 Fita ma putati nu yen kokul uh oan we pa elos su lohg — a elya lalos, ac mwe kasrup ac mwe pwar lun moul se inge ekosla acn sin kas uh, na fahko uh tiana mwesrla.
Irin da suka fada cikin kayayuwa, sune mutanen da suka ji maganar, amma da suka ci gaba da rayuwa, sai suka bari matsalolin rayuwa kamar dukiya da jin dadin rayuwa suka fi karfinsu, sai ya zama ba su iya bada 'ya'yan da suka yi girma ba.
15 Fita ma putati in fohk wo uh pa mwet su lohng kas uh, ac sang nu insielos ke nunak wo ac akosten. Ac elos sruokya ku nwe ke na isus fahko.
Amma irin da suka fada a kan kasa mai kyau, wadannan sune mutanen da suka ji maganar, suka karbe ta da gaskiya da zuciya daya, sun rike ta kam-kam, suna jimrewa wurin ba da 'ya'ya.
16 “Wangin sie mwet ac akosak lam uh ac filiya ye sie ahlu ku ye sie bed, a el ac filiya fin sukan lam uh, tuh mwet in liye kalem uh ke elos ac utyak nu in lohm uh.
Ba mai kunna fitila, ya rufe ta da kasko, ko su sa ta a karkashin gado. Amma sai a sa ta a wurin zaman ta domin duk wanda ya shigo ya iya ganin hasken ta.
17 “Kutena ma su wikla ac fah liyeyuk lemtulauk sin mwet uh, ac kutena ma su lukmaiyuk, ac fah akkalemyeyuk.
Babu abin da yake a boye wanda ba za a tone shi ba, ko wani asiri da ba za ya fito fili a san shi ba.
18 “Ke ma inge, kowos lohng akoaruye, mweyen el su oasr ma yoro, ac fah itukyang pac kutu nu sel; a el su wangin ma yoro, ac fah itukla lukel, finne ma srisrik ma el nunku mu oasr yorol.”
Ku yi hankali da yadda kuke ji, domin duk mai abu, shi za a kara wa, kuma duk mara abu, dan kadan da yake tunani yana da shi ma, za a dauke.”
19 Nina kial Jesus ac tamulel lal elos tuku nu yorol, tusruktu ke sripen iktokeni lun mwet uh, elos tia ku in kalukyang nu yorol.
Sai mahafiyar Yesu da 'yan'uwansa, su ka zo wurinsa, amma ba su iya zuwa ko kusa da shi ba saboda taron jama'a.
20 Sie sin mwet uh fahk nu sel Jesus, “Nina kiom ac tamulel lom ah pa tu likinum uh, ac elos ke osun nu sum.”
Sai wani ya gaya masa, “Ga mahaifiyarka da 'yan'uwanka, su na tsayuwa a waje, su na son ganin ka.”
21 Jesus el fahk nu selos nukewa, “Nina kiuk ac mwet lik uh pa elos su lohng kas lun God ac akos.”
Amma Yesu ya amsa ya ce ma su, “Mahaifiyata da 'yan'uwana sune wadanda suke jin maganar Allah, suke yin biyayya da ita.”
22 Sie len ah Jesus el sroang nu fin oak soko wi mwet tumal lutlut, ac el fahk nu selos, “Kut kalot nu lefahlo.” Na eltal oacla.
Wata rana kuma Yesu ya shiga cikin jirgin ruwa, shi da almajiransa. Ya ce masu, “Ina so mu je dayan ketaren tafkin.” Sai su ka fara tafiya domin su ketare tafkin.
23 Ke elos kalkalla in lulu uh, Jesus el motulla. Kitin pacl ah na eng na upa se tuhyak ac oak uh mutawauk in sessesla ke kof, ac elos nukewa arulana fosrngala.
Amma sa'adda su ke tafiya sai Yesu ya yi barci, sai wata iska mai karfi ta taso cikin tafkin, nan da nan sai jirgin ya fara cika da ruwa, kuma su na cikin hatsari.
24 Mwet tumal lutlut elos som ac oaksalak Jesus ac fahk, “Leum, Leum! Kut ac misa pa’nge!” Jesus el tukakek ac kai eng upa sac ac noa uh, na eng uh mihsi ac noa uh tui, ac mihs na lulap se sikyak.
Sai almajiran Yesu su ka zo su ka tashe shi daga barci. Suka ce da shi, “Ya Shugaba! Ya Shugaba! Za mu mutu!” Sai ya tashi ya umarci iskar, sai iskar mai hauka da tumbatsar ruwan sun tsaya tsit.
25 Na el fahk nu sin mwet tumal lutlut, “Pia lulalfongi lowos an?” A elos arulana fwefela ac sangeng, ac fahk nu sin sie sin sie, “Su mwet se inge? El sapsap nu sin eng uh ac noa uh, ac elos aksol!”
Daga nan sai ya ce da su, “Ina bangaskiyar ku?” Almajiran suka tsorata suka yi mamakin abin da ya faru nan take. Suka ce wa junansu, “Wanene wannan wanda har zai ba iska da ruwa umarni kuma su yi masa biyayya?”
26 Jesus ac mwet tumal lutlut elos kalla na som nu Gerasa, su oan lefahl laco in lulu uh tulanya acn Galilee.
Suka zo yankin Garasinawa, wanda ke kusa da Gallili.
27 Ke Jesus el srola nu finmes uh, el sun mwet se in acn sac su oasr ngun fohkfok pus in el. Ke lusen pacl na loes se mwet se inge tiana nuknuk, ac tia muta lohm sel, a el mutana inmasrlon kulyuk uh.
Sa'adda Yesu ya sauka kasa, sai wani mutum daga wannan yankin ya tarbe shi. Wannan mutum kuwa yana da aljanu. Mutumin ya dade ba ya sa tufafi, kuma ba ya zama a gida. Maimakon haka, sai a cikin kabarbura ya ke zama.
28 Ke el liyalak Jesus, el wowoyak ac putati nu ke nial, ac fahk ke sie pusra lulap, “Jesus, Wen nutin God Fulatlana! Mea kom lungse sik an? Nga kwafe sum, nimet akkeokyeyu!”
Sa'adda ya ga Yesu, mutumin ya yi ihu da karfi, ya rusuna a gabansa da babban murya ya ce, “Me zan yi da kai, Yesu, Dan Allah Madaukaki? Ina rokonka, kada ka ba ni azaba!”
29 El fahk ma inge mweyen Jesus el tuh sap ngun fohkfok sac in som lukel. Pacl na pus ngun fohkfok sac sruokilya, ac el nwe sruhu in presin ac paol ac nial kapiri na ke sein, a el ac wotyalik sein inge, ac ngun fohkfok sac ac kololla nu yen mwesis.
Domin Yesu ya umarci aljanun su fita daga cikinsa, domin sau da dama aljanun sukan kama shi. Ko an daure mutumin da sarkoki an kuma tsare shi, yakan tsuttsunke su, kazaman ruhohin sukan kora shi cikin jeji.
30 Jesus el siyuk sel, “Su inem an?” El fahk, “Inek pa ‘Legion’”— mweyen pus na ngun fohkfok ilyak tari nu in el.
Sa'annan Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Sai ya ba da amsa, “Suna na dubbai.” Ya ce haka ne domin aljanu da yawa sun shiga wannan mutum.
31 Ngun fohkfok uh kwafe sel Jesus elan tia luselosla nu in luf loal wangin saflaiya. (Abyssos g12)
Aljanun suka yi ta rokon Yesu kada ya ummarce su su shiga cikin rami mai zurfi. (Abyssos g12)
32 Tuh oasr un pig na lulap se muta in acn sac mongo pe eol uh. Ouinge ngun fohkfok uh kwafe tuh Jesus elan fuhlelosla elos in ilyak nu in pig uh, na el fuhlelosla.
Akwai babban garken aladu su na kiwo a kan tsauni kusa da wurin. Aljanun suka roki Yesu da ya barsu su shiga cikin aladun, shi kuwa ya yarda masu.
33 Elos illa liki mwet sac nu in pig uh. Na un pig na fon sac riryak som liki mutun fulu sac ac atula nu in kof uh ac walomla.
Aljanun suka bar mutumin suka shiga cikin aladun, sai garken aladun suka gangara kwari suka fada cikin tafkin, suka nutse.
34 Mwet ma karingin un pig uh liye ma sikyak uh, na elos kasrusr som ac fahkelik pweng sac in siti uh ac yurin mwet orek ima uh.
Lokacin da mutanen da su ke kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka gudu! Suka ba da rahoton abin da ya faru ga mutanen cikin gari da na wannan kewayen.
35 Mwet uh som in liye ma sikyak inge, ac ke elos tuku nu yurin Jesus elos liyauk mwet se ma ngun fohkfok uh itukla lukel lah el muta ke nien Jesus — el nuknukyang ac tila wel; ac elos nukewa arulana sangeng.
Don haka, mutanen da suka ji haka suka tafi domin su ga abin da ya faru, suka zo wurin da Yesu yake, suka ga mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa. Suka ga ya na sanye da tufafi, kuma ya na cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Mwet ma liye ma inge elos fahkak ouiyen kwela lun mwet sac liki mas lal.
Mutanen da suka ga abin da ya faru, suka gaya wa wadansu yadda aka warkar da mutumin da aljanu suke iko da shi.
37 Na mwet nukewa in acn Gerasa siyuk Jesus elan som liki acn we, mweyen elos nukewa arulana sangeng. Ouinge Jesus el sroang nu fin oak uh in som.
Sai dukan mutane wadanda suke cikin yankin Garasinawa da wadanda suke kewaye, suka roki Yesu da ya fita daga cikin yankin kasarsu domin sun ji tsoro kwarai da gaske. Daga nan Yesu da almajiransa suka shiga cikin jirgin ruwa suka koma.
38 Mwet se ma ngun fohkfok uh som lukel el kwafe nu sin Jesus ac fahk, “Nga ku in wi kom som?” A Jesus el fahk,
Mutumin wanda aljanu suka fita daga cikinsa, ya roki Yesu cewa, “Ka barni in tafi tare da kai!” Amma Yesu ya sallame shi cewa,
39 “Folokla nu in acn sum ac fahkak ma nukewa ma God El oru nu sum.” Na mwet sac fahsr sasla in siti sac, ac fahkak ke ma nukewa Jesus el oru nu sel.
“Ka koma gida ka gaya wa mutanen ka abubuwa masu girma wadanda Allah ya yi maka.” Daga nan sai mutumin ya tafi yana ta gayawa dukan mutanen birnin game da abubuwan da Yesu ya yi masa.
40 Ke Jesus el foloko mwet uh insewowo in paingul, mweyen elos nukewa muta soanel.
Sa'adda Yesu ya dawo, mutanen suka marabce shi, gama, dukansu suna jiransa.
41 Na mwet se pangpang Jairus el tuku — el sie mwet kol lun iwen lolngok we. El putati nu ke nien Jesus, ac kwafe sel elan som nu lohm sel ah,
Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, daya daga cikin shugabannin majami'a, ya zo kusa da Yesu ya rusuna da kansa a kasa. Ya roke shi domin ya zo gidansa,
42 mweyen acn sefanna natul su yac singoul luo matwal, el mas ac apkuran in misa. Ke Jesus el welul som, u lulap sac ukwalla pac, oru elos arulana iktokeni.
saboda diyarsa mai kimanin shekara goma sha biyu ta na bakin mutuwa, kuma ita kadai ce diya a gare shi. Amma sa'adda yake tafiya, taron mutane da yawa suna matsa shi.
43 Oasr pac sie mutan wi un mwet sac fahsr su maskin musen srah ke yac singoul luo. El sisla mani lal nukewa nu sin mwet ono, tuh wanginna sie ku in akkeyalla.
Akwai wata mace a nan wadda take zubar jini har shekara goma sha biyu. Ta kashe kudinta duka a wurin likitoci, domin su warkar da ita amma ba wanda ya iya warkar da ita.
44 El fahsryak inmasrlon mwet uh nu tokol Jesus ac kahlye pulan nuknuk lal ah, ac kitin pacl ah na musen srah se lal ah tui.
Sai ta biyo ta bayan Yesu ta taba habar rigarsa. Nan take sai zubar jinin ya tsaya.
45 Na Jesus el fahk, “Su kahlyuwi uh?” Mwet nukewa fahk mu tia etu, na Peter el fahk, “Leum, mwet uh arulana raunikomla ac ikuskomyak.”
Yesu ya ce, “Wanene ya taba ni?” Wadanda suke kewaye da shi, kowa ya ce bai taba shi ba, Bitrus ya ce, “Shugaba, mutane da yawa suna ta taruwa kewaye da kai suna ta matsowa kusa da kai.”
46 A Jesus el fahk, “Oasr mwet se kahlyuwi, mweyen nga pula mu oasr ku luk som likiyu.”
Amma Yesu ya ce, “Na sani, wani ya taba ni, domin iko ya fita daga wurina.”
47 Mutan sac akilen lah eteyukyak ma el oru uh, ouinge el fahsryak rarrar ac putati nu ke nien Jesus. Ye mutun mwet nukewa el fahkak nu sel lah efu ku el kahlilya, ac fahk pac lah mas lal wanginla in pacl sacna.
Sa'adda matar ta gane cewa ba za ta iya boyewa ba, sai ta zo wurinsa cikin tsoro. Ta durkusa a gaban Yesu, ta fada a gaban dukan jama'a dalilin da ya sa ta taba shi kuma nan da nan ta warke.
48 Jesus el fahk nu sel, “Acn nutik, lulalfongi lom akkeyekomla. Som in misla.”
Sai ya ce da ita, “Diya, bangaskiyarki ta warkar da ke. Tafi cikin salama.”
49 Ke Jesus el srakna fahk ma inge, sie mwet supweyukme liki lohm sin mwet kol lun iwen lolngok sac ac fahk nu sel, “Jairus, acn nutum el misa. Nimet sifil aklokoalokye mwet luti sacn.”
Yana cikin yin magana, wani daga cikin gidan shugaban majami'ar ya zo, ya ce, “Diyarka ta riga ta mutu, kada ka dami malam.”
50 Tusruk Jesus el lohng sap soko ah, ac el fahk nu sel Jairus, “Nikmet fosrnga. Lulalfongi na, ac tulik sac ac fah sifil moul.”
Amma sa'adda Yesu ya ji haka, sai ya ce da shi, “Kada ka ji tsoro. Ka bada gaskiya za ta rayu.”
51 Ke Jesus el sun lohm sac, el tia lela kutena mwet in welul utyak sayal Peter, John, ac James, oayapa papa ac nina kien tulik sac.
Sa'adda ya zo gidan, bai bar kowa ya shiga gidan tare da shi ba sai Bitrus da Yahaya da Yakubu, da mahaifiyar yarinyar da babanta.
52 Mwet in lohm sac nufon elos tung ac asor ke tulik sac. Ac Jesus el fahk, “Nimet kowos tung. Tulik se inge tia misa, el motul na!”
Dukan mutane a wurin, suna ta kuka da karfi saboda sun damu da yarinyar ta mutu. Amma Yesu ya ce da su, “Ku dena kuka! Ba mutuwa ta yi ba! Barci ta ke yi kawai!”
53 Elos nukewa isrunul, mweyen elos etu lah tulik sac misa tari.
Mutanen suka yi ma sa dariyan reni, saboda sun sani yarinyar ta mutu.
54 A Jesus el sruokya paol ac fahk ke pusra lulap, “Tulik se, tukakek!”
Amma ya kama hannun ta yayi kira cewa, “Yarinya, na ce ki tashi!”
55 Na el moulyak, ac in kitin pacl ah na el tukakek, ac Jesus el sap elos in sang kutu mongo nal.
Nan da nan ruhun ta ya dawo jikin ta sai ta tashi. Ya ce masu su ba ta wani abu ta ci.
56 Papa ac nina kial eltal arulana lut, tusruk Jesus el fahk eltal in tiana fahk nu sin kutena mwet ma sikyak uh.
Iyayenta suka yi mamaki, amma Yesu ya ce da iyayen kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >