< Orekma 1 >

1 Nu sum, Theophilus: In book se luk meet ah, nga tuh simusla ma nukewa su Jesus el tuh oru ac luti nu sin mwet uh ke el mutawauk orekma lal
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 nwe ke na sun len se ma tuh utukyak el nu inkusrao. Meet liki utukyak el, ke ku lun Ngun Mutal el sang kas lal nu sin mwet el tuh sulela in mwet sap lal.
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 Ke lusen len angngaul tukun el misa, el tuh sikyang nu selos pacl na pus in ouiya su liksreni na akpwayei lah pwaye el sifil moulyak. Elos liyal, ac el kaskas nu selos ke Tokosrai lun God.
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 Ac ke el srakna muta yorolos, el fahk sap soko inge nu selos: “Nimet som liki acn Jerusalem, a kowos in soano na mwe kite se su nga tuh fahk nu suwos, su Papa El wulela kac.
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 John el tuh baptais ke kof, a in len ekasrna fahsru, kowos ac fah baptais ke Ngun Mutal.”
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 Ke mwet sap elos tukeni nu yurin Jesus, elos siyuk sel, “Leum, ya kom ac folokonak tokosrai lun mwet Israel ke pacl se inge?”
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 Jesus el fahk nu selos, “Pacl uh, ac ma ac orek uh, oakwuk ke ku lun Papa tumuk, ac tia ma lowos in etu lah ma inge ac sikyak ngac.
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8 Tusruktu kowos ac fah eis ku ke Ngun Mutal ac tuku nu fowos, ac kowos ac fah mwet loh keik in acn Jerusalem, ac in acn Judea nufon, oayapa Samaria, ac nu in acn nukewa fin faclu.”
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 Tukun el fahk ma inge tari, utukyak el nu inkusrao ye mutalos, na pukunyeng se kosralla lukelos.
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 Elos srakna suiya acn lucng ke utukyak el ah, na mwet luo sikme welulosyang, nukum nuknuk na fasrfasr
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 ac fahk, “Mwet Galilee, efu kowos tu nget na nu lucng? Jesus se ma utukla liki kowos nu inkusrao inge, ac fah sifilpa foloko in lumah se na ma kowos liye el som nu inkusrao kac ah.”
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Na mwet sap elos folokla nu Jerusalem liki fineol Olive, su lusa oasr ke tafun mael.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 Elos folokla nu in siti uh, ac utyak nu in lohm se elos muta we ah: Peter, John, James ac Andrew, Philip ac Thomas, Bartholomew ac Matthew, James wen natul Alphaeus, Simon mwet Zealot, ac Judas wen natul James.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 Elos inge kwacna tukeni nu sie in pre, wi mutan uh, ac Mary nina kien Jesus, ac mukul wial ah.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 In kutu len tok, un mwet lulalfongi elos toeni — sahp ac oasr mwet siofok longoul nufon — na Peter el tuyak in sramsram.
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 El fahk, “Mwet lili ac lulu, ac nuna akpwayeiyuk Ma Simusla se ma fahk ke Ngun Mutal tuh palye in kas lal David, ke ma ac sikyak kacl Judas, mwet se ma pwanulos su sruokilya Jesus ah.
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 Judas el tuh sie sesr, ke sripen solla el in wi ipeis ke orekma se inge.”
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 (Mani se ma Judas el tuh eis ke sripen ma koluk se ma el orala, el sang molela sie ipin acn. Acn sacna pa el tuh putatla ac misa we, ac sial fokelik ac koanonsial nufon raki.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 Mwet nukewa su muta Jerusalem elos lohng ke ma inge, ouinge in kas lalos sifacna elos pangon ipin acn sac Akeldama, su kalmac pa “Acn Moulla ke Srah.”)
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 “Tuh simla in book in Psalm, ‘Lela lohm sel in pisinmala; Ac in wangin mwet muta we,’ Oayapa simla mu, ‘Lela siena mwet in eis orekma lal.’
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 “Ke ma inge enenu na tuh sie sin mwet ma wi kut na fufahsryesr ke pacl Jesus el muta yorosr,
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 mutawauk na oe ke pacl ma John el tuh fahkak mwe luti lal ke baptais, nwe ke utukyak Jesus liki kut nu inkusrao. Mwet ouinge se pa enenu in wikutyang in orek loh ke moulyak lun Jesus Christ.”
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 Ouinge elos sulela mwet luo: Joseph (su pangpang pac Barsabbas ku Justus), ac Matthias.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 Na elos pre ac fahk, “O Leum, kom etu nunak lun mwet nukewa. Ke ma inge, ikasla nu sesr lah su sin mwet luo inge kom sulela
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
25 in eis orekma lun mwet sap in aolul Judas, su som tari nu in acn fal nu sel.”
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 Tari na elos susfa ke mwet luo inge, ac oayang nu sel Matthias, su weang mwet sap singoul sie ah.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.

< Orekma 1 >