< Mathayo 21 >

1 Yesu na abheigisibhwa bhaye nibhakinga yei na Yerusalemu nibhagenda okukinga Bhetifage, kuchima cha Mijeituni, nio Yesu namala nabhatuma abheigisibhwa bhabhili, nabhabhwila ati,
Da suka yi kusa da Urushalima suka kuma kai Betfaji da yake kan Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajirai biyu,
2 “Mugende muchijiji echo echilubhila, mchali kubhusha mwanya omusanga insikiri isibhikilwe ao na akana kayo. Mujisulumule na mujilete kwanye.
yana ce musu, “Ku je ƙauyen da yake gabanku, nan take za ku ga wata jaka a daure tare da ɗanta kusa da ita, a can. Ku kunce su ku kawo mini.
3 Labha omunu wona wona akabhabhusha chona chona ingulu yo musango ogwo, mwaike ati, 'Omukama kajenda,' na omunuyo obhutabhusha mwanya kabhayana omwanya muje najo.”
In wani ya yi muku wata magana, ku ce masa Ubangiji yana bukatarsu, zai kuwa mai da su nan da nan.”
4 Ligambo linu lyejile lwa kutyo lyaikilwe okulabha ku mulagi, Ni bhusibhusi likumile. Lwakutyo aikile ati,
Wannan ya faru ne don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabin cewa,
5 Bhabhwile abhaasha bha Sayuni, Lola, Omukama wao kaja kwimwe, Ekeyishe na alinyile insikiri, eye chinyara chilume, echinyara ch ilela.
“Ku ce wa Diyar Sihiyona, ‘Duba, sarkinki yana zuwa gare ki, mai tawali’u yana a kan jaki, a kan aholaki, ɗan jaki.’”
6 Nibheya abheigisibhwa nibhagenda nibhakola kutyo Yesu abhalagiliye.
Almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 Nibhaleta insikiri na omwana gwayo, nibhanja emyenda jebhwe kumigongo ja jinsikiri, Yesu neyanjako.
Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa mayafansu a kansu, Yesu kuma ya zauna a kansu.
8 Abhanu bafu nibhanja emyenda jebhwe munjila, abhandi nibhatema amatabhi ga mati no kuganja munjila.
Wani babban taron mutane suka shimfiɗa mayafansu a kan hanya, yayinda waɗansu suka sassari rassan itatuwa suka shisshimfiɗa a kan hanya.
9 Abhanu bhanu bhaliga bhatandikile na bhanu bhaliga nibhasoka inyuma nibhasekana nibhaika ati Hosana ku mwana wa Daudi! Ayanilwe amabhando ejile kwisina lyo Omukama. Hosana abhe ingulu muno!
Taron mutanen da suke gabansa da kuma waɗanda suke binsa a baya suka yi ihu suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” “Mai albarka ne wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Hosanna a cikin sama!”
10 Yesu ejile akinga Yerusalemu, echikale chona nichitinyuka nichaika ati Unu niga?
Sa’ad da Yesu ya shiga Urushalima, dukan birnin ya ruɗe, ana ta tambaya, “Wane ne wannan?”
11 “Liijo lya abhanu nilisubhya ati, “Unu ni Yesu Omulagi, okusoka Nazareti ya Galilaya.”
Taron mutane suka amsa, “Wannan shi ne Yesu, annabin nan daga Nazaret a Galili.”
12 Yesu namala nengila muyekalu lya Nyamuanga. Nabhabhilimya bhasokemo bhona bhanu bhaliga nibhagusha nokugula ebhinu muyekalu. Nagalamula jimeja ja bhanu bhaingyaga jimpilya ne bhitebhe bhya abhagusha bha jinjibha.
Yesu ya shiga filin haikali, ya kuma kori duk masu saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur masu canjin kuɗi da kuma kujerun masu sayar da tattabarai.
13 Nabhabhwila ati, “Jandikilwe”, 'Inyumba yani ilitogwa Inyumba ya lisabhwa,' nawe emwe mwaikolele kubha 'eyata lya bhefi'”
Ya ce musu, “A rubuce yake, ‘Za a ce da gidana, gidan addu’a,’amma kuna mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
14 Nio abhalema na abhaofu nibhamulubha mwiyekalu, omwene nabhaosha.
Makafi da guragu suka zo wurinsa a haikali, ya kuwa warkar da su.
15 Nawe abhakulu bha abhagabhisi na abhandiki bhejile bhalola ebhilugusho ebhyo akolele, na bhejile bhongwa abhana nibhayoganila mwiyekalu nibhaikaga ati, “Hosana ku Mwana wa Daudi,” nibhagwatwa nebhinyiga.
Amma da manyan firistoci da malaman dokoki suka ga abubuwan banmamakin da ya yi, yara kuma suna ihu a filin haikali suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda,” sai fushi ya kama su.
16 Nibhamubhwila ati, “Oungwa chinu echaikwa na abhanu bhanu?” Yesu nabhabhwila ati, “Yee! Mbe nawe muchaliga kusoma, okusoka muminwa ja abhana na abhana abhalela wanu abhanena galimo amakumusho ganu gengene.”
Suka tambaye shi suka ce, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, ba ku taɓa karanta ba cewa, “‘Daga leɓunan yara da jarirai kai, Ubangiji, ka shirya wa kanka yabo’?”
17 Neya Yesu nabhasiga nagenda Betaniya anja yo omusi namama eyo.
Sai ya bar su, ya fita daga birnin ya tafi Betani, inda ya kwana.
18 Ao aliganasubha muchikale katondo, aliga alinomweko.
Kashegari da sassafe, yayinda yake kan hanyarsa ta komawa cikin birni, sai ya ji yunwa.
19 Mbe nalola liti elyo mtini kungego ya injila. Nalijako, nawe atabhweneko chinu chonachona tali amabhabhi genyele. Nalibhwila ati, “Utasubha kutwasha amatwasho lindi.” Akatungu akwako litini elyo nilyuma. (aiōn g165)
Ganin itacen ɓaure kusa da hanya, sai ya je wajensa amma bai sami kome a kansa ba sai ganye. Sai ya ce masa, “Kada ka ƙara yin’ya’ya!” Nan da nan itacen ya yanƙwane. (aiōn g165)
20 Abheigibhwa bhejile bhalola kutyo nibhalugula nokwaika ati, “Jabha kutiki okukingila omutini gume lugendo lumwi?”
Sa’ad da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya itacen ɓauren ya yanƙwane nan da nan haka?”
21 Yesu nabhasubhya kwokubhabhwila ati, “Ni chimali enibhabhwila ati, labha mkabha muli nelikilisha mtali na wasiwasi, mutalikola linu lyakolekana ku mutini ogwo ela, nawe mulibhwila nolwo echima echo, 'nugegwe na ulaswe munyanja,' na elikolekana.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiya, ba kuwa da wata shakka ba, ba kawai za ku iya yin abin da aka yi wa itacen ɓauren nan ba, amma za ku ma iya ce wa dutsen nan, ‘Je ka, ka jefa kanka cikin teku,’ sai yă faru.
22 Lyonalyona elyo mulisabhwa, enu mwikilisishe, omulamila.”
In kun gaskata, za ku karɓi duk abin da kuka roƙa a cikin addu’a.”
23 Yesu ejile akakinga mwiyekalu, abhakulu bha abhagabhisi na abhakaruka bha imbaga nibhamujako ao aliga neigisha nibhamubhusha ati, “Oukola amagambo ganu kwa bhutolo bhwa namunaki?”
Sai Yesu ya shiga filin haikali, yayinda yake koyarwa, sai manyan firistoci da dattawan mutane suka zo wurinsa suka yi tambaya, “Da wane iko kake yin waɗannan abubuwa? Kuma wa ya ba ka wannan iko?”
24 Yesu nabhasubhya nokubhabhusha ati, “Anyona enibhabhusha libhusho limwi, labha mkambwila, anyona omwomwo enibhabhwila enikola amagambo ganu kwa bhutuloki.
Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku tambaya guda. In kuka ba ni amsa, ni ma zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa.
25 “Ubhubhatijo bhwa Yoana bhwasokele aki, mulwire amo kubhana bhanu?” Nibhabhushanya abhene kwa bhene, nibhaika, “chikaika ati bhwasokele mulwire, kaja okuchibhwila ati kubhaki mutamwikilisishe?
Baftismar Yohanna, daga ina ta fito? Daga sama ce, ko daga mutane?” Sai suka tattauna a junansu suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama,’ zai ce, ‘To, me ya sa ba mu gaskata shi ba?’
26 Nawe chikaika ati bhwasokele kubhana bhanu, mbe chubhaye abhanu kulwokubha bhona bhanu abhalola nkanikwo Yoana ni mulagi.”
In kuma muka ce, ‘Daga mutane,’ muna tsoron mutane, gama duk sun ɗauka Yohanna annabi ne.”
27 Ni bhamala nibhamusubhya Yesu nibhaika ati, “Chitakumenya.” Omwene on nabhasubhya ati, “Nolwo anye ona nitabhabhwila amanaga ganu enikolela amagambo ganu.”
Saboda haka suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Sai ya ce, “Ni ma ba zan gaya muku ko da wane iko nake yin waɗannan abubuwa ba.”
28 “Nawe omwiganilisha kutiki? Aliga alio omunu umwi ali nabhana bhabhili. Mbe nagenda kuwokwamba namubhwila ati, 'Mwana wani, lelo genda ukole emilimu mwisambu lye emijabhibhu.'”'Omwana waye namusubhya ati,
“Me kuka gani? An yi wani mutum wanda yake da’ya’ya biyu maza. Sai ya je wajen ɗan farin ya ce, ‘Ɗana, yau tafi gonar inabi ka yi aiki.’
29 'Nitakujayo.' Nawe namala naindula omwoyo gwaye nagenda.
“Ya amsa ya ce, ‘Ba zan tafi ba,’ amma daga baya ya sāke tunani, ya tafi.
30 Omunu oyo nagenda ku mwana wakabhili namubhwila lwakutyo abhwiliye owo kwamba. Unu namubhwila ati, 'Enigenda, lata,' nawe atagendele.
“Sai mahaifin ya tafi waje na biyun ya faɗa masa iri magana guda. Sai ya amsa ya ce, ‘Zan tafi, ranka yă daɗe,’ amma bai tafi ba.
31 “Mbe niga Unu akolele ejo esemwene aliga nenda.” Nibhasubya ati, “Omwana wo kwamba.” Yesu nabhabhwila ati, “Enibhabhwila echimali abhatobhesha bha ligoti na abhasimbe bha mubhilabho bhalibhelabhila okwingila mubhukama bhwa Nyamuanga.
“Wanne cikin yaran nan biyu ya yi abin da mahaifinsa yake so?” Suka amsa, “Na farin.” Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga mulkin Allah.
32 Kulwokubha Yoana ejile kunjila igololokele, nawe mutamwikilisishe, ka abhatobhesha bha ligoti na abhasimbe bha mubhilabho nibhamwikilisha. Emwe mwejile mwalola echo kutyo, nimusingwa okuta ebhibhi koleleki mumwikilishe.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo wurinku don yă nuna muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba, amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata. Har ma bayan kun ga wannan, ba ku tuba kun gaskata shi ba.”
33 Mbe mutegeleshe echijejekanyo echindi. Aliga aliwo omunu ali na lisambu enene. Aliga ayambile emijabhibhu, asingilisishe olugo, ateyemo na litwangilo lyokukamulila idivai, ombakilemo no olugujo lwa abhalindi na alikodesishe lisambu kubhanu bhanu abhalyangalila. Namala nasokao nagenda muchalo chindi.
“Ku saurari wani misali. An yi wani mai gona wanda ya yi gonar inabi. Ya kewaye ta da katanga, ya haƙa wurin matsin inabi a ciki, ya kuma gina hasumiyar gadi. Sa’an nan ya ba wa waɗansu manoma hayar gonar inabin, ya kuma yi tafiya.
34 Akatungu akokunogola amatwasho get emijabhibhu kejile kakinga, nabhatuma abhakosi bhandi kubhalimi bhe emijabhibhu koleleki bhamugegele amatwasho gaye.
Da lokacin girbi ya yi kusa, sai ya aiki bayinsa wajen’yan hayan, su karɓo masa’ya’yan inabi.
35 Nawe abhalimi bhe emijabhibhu nibhabhagega abhakosi bhaye, nibhamubhuma oumwi webhwe, oumwi nibhamwita no oundi nibhamulasa na amabhui.
“Amma’yan hayan suka kama bayinsa; suka dūke ɗaya, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi na ukun.
36 Olugendo lundi, nasubha okutuma abhakosi bhandi bhafu okukila abhokwamba, nawe abhalimi bhe emijabhibhu nibhabhakolela amabhibhi lwa bhaliya.
Sai ya sāke aiken waɗansu bayi wurinsu, fiye da na dā yawa, amma’yan hayan suka yi musu kamar yadda suka yi wa na farin.
37 Nio neya nalamula natuma omwana waye, naika ati, 'Abhamuyana echibhalo omwana wani.'
A ƙarshe, sai ya aiki ɗansa a wurinsu. Ya ce, ‘Za su girmama ɗana.’
38 Nawe bhejile bhamulola omusigaji oyo, nibhaikana ati, 'Unu niwe kalya omwandu, Muje chimwite chigege omwandu.'
“Amma da’yan hayan suka hangi ɗan, sai suka ce wa juna, ‘Wannan shi ne magājin. Ku zo, mu kashe shi, mu ci gādonsa.’
39 Kulwejo nibhamugega, nibhamulasa anja ya lisambu lye emijabhibhu nibhamwita.
Saboda haka suka kama shi, suka jefar da shi bayan katangar gonar inabin, suka kashe shi.
40 Mbe enibhusha, Kanye esambu elye mijabhibhu alibha aja, alibhakolela abhalimi abho?”
“To, idan mai gonar inabin ya zo, me zai yi da’yan hayan nan?”
41 Nibhamubhwila ati, “alibhasingalisha abhanyamuke abho kwa lisungu enene, akamala natisha lisambu kubhalimi abhandi abhe emijabhibhu, bhanu bhalibha a nibhaliila emijabhibhu akatungu kokuisha.”
Suka amsa suka ce, “Zai yi wa banzan mutanen nan mugun kisa, yă ba da hayar gonar inabin ga waɗansu’yan haya, waɗanda za su ba shi rabonsa na amfanin gona a lokacin girbi.”
42 Mbe Yesu nabhabhwila ati, “Mutasomele Amandiko amelu, 'libhui linu bhalemele abhombaki nilibha ebhui enene elyo omusingi. Linu lyasokele ku Mukama, na elilugusha ameso geswe?”
Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta a cikin Nassi cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi shi ne ya zama dutsen kusurwar gini. Ubangiji ne ya aikata wannan, kuma abin mamaki ne a idanunmu’?
43 Kulwejo enibhabhwila kutiya, Obhukama bhwa Mungu bhuligegwa okusoka kwemwe nibhayabhwa liyanga linu elimenya amatwasho go obhukama obhwo.
“Saboda haka, ina gaya muku cewa za a karɓe mulkin Allah daga gare ku, a ba wa mutanen da za su ba da amfani.
44 Wona wona unu kagwa kwibhui elyo kabhutuka mabhala bhala.”
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Amma duk wanda dutsen nan ya fāɗi a kansa, za a murƙushe shi.”
45 Mbe abhakulu bha abhagabhisi na abhafarisayo bhejile bhongwa ebhijejekanyo bhaye, ni bheyungwa ati kalomelela abhene.
Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan Yesu, sai suka gane cewa da su yake.
46 Nawe ao bhendelaga okumugwata, bhobhayaga liijo lya abhanu, kulwokubha abhanu bhamulolaga kuti ni mulagi.
Suka nemi hanyar kama shi, amma suka ji tsoron taron, don mutane sun ɗauka shi annabi ne.

< Mathayo 21 >