< Salmi 81 >

1 Per il Capo de’ musici. Sulla Ghittea. Salmo di Asaf. Cantate con gioia a Dio nostra forza; mandate grida di allegrezza all’Iddio di Giacobbe!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Intonate un salmo e fate risonare il cembalo, l’arpa deliziosa, col saltèro.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Sonate la tromba alla nuova luna, alla luna piena, al giorno della nostra festa.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Poiché questo è uno statuto per Israele, una legge dell’Iddio di Giacobbe.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Egli lo stabilì come una testimonianza in Giuseppe, quando uscì contro il paese d’Egitto. Io udii allora il linguaggio di uno che m’era ignoto:
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 O Israele, io sottrassi le tue spalle ai pesi, le tue mani han lasciato le corbe.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Nella distretta gridasti a me ed io ti liberai; ti risposi nascosto in mezzo ai tuoni, ti provai alle acque di Meriba. (Sela)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Ascolta, o popolo mio, ed io ti darò degli ammonimenti; o Israele, volessi tu pure ascoltarmi!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Non vi sia nel mezzo di te alcun dio straniero, e non adorare alcun dio forestiero:
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Io sono l’Eterno, l’Iddio tuo, che ti fece risalire dal paese d’Egitto; allarga la tua bocca, ed io l’empirò.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Ma il mio popolo non ha ascoltato la mia voce, e Israele non mi ha ubbidito.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Ond’io li abbandonai alla durezza del cuor loro, perché camminassero secondo i loro consigli.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Oh se il mio popolo volesse ascoltarmi, se Israele volesse camminar nelle mie vie!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Tosto farei piegare i loro nemici, e rivolgerei la mia mano contro i loro avversari.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Quelli che odiano l’Eterno dovrebbero sottomettersi a lui, ma la loro durata sarebbe in perpetuo.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 Io li nutrirei del fior di frumento, e li sazierei di miele stillante dalla roccia.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Salmi 81 >