< Salmi 105 >

1 Celebrate l’Eterno, invocate il suo nome; fate conoscere le sue gesta fra popoli.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Cantategli, salmeggiategli, meditate su tutte le sue maraviglie.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Gloriatevi nel santo suo nome; si rallegri il cuore di quelli che cercano l’Eterno!
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Cercate l’Eterno e la sua forza, cercate del continuo la sua faccia!
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Ricordatevi delle maraviglie ch’egli ha fatte, de’ suoi miracoli e dei giudizi della sua bocca,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 o voi, progenie d’Abrahamo, suo servitore, figliuoli di Giacobbe, suoi eletti!
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Egli, l’Eterno, è l’Iddio nostro; i suoi giudizi s’esercitano su tutta la terra.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Egli si ricorda in perpetuo del suo patto, della parola da lui data per mille generazioni,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 del patto che fece con Abrahamo, del giuramento che fece ad Isacco,
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 e che confermò a Giacobbe come uno statuto, ad Israele come un patto eterno,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 dicendo: Io ti darò il paese di Canaan per vostra parte di eredità.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Non erano allora che poca gente, pochissimi e stranieri nel paese,
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 e andavano da una nazione all’altra, da un regno a un altro popolo.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Egli non permise che alcuno li opprimesse; anzi, castigò dei re per amor loro
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 dicendo: Non toccate i miei unti, e non fate alcun male ai miei profeti.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Poi chiamò la fame sul paese, e fece mancar del tutto il sostegno del pane.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Mandò dinanzi a loro un uomo. Giuseppe fu venduto come schiavo.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 I suoi piedi furon serrati nei ceppi, ei fu messo in catene di ferro,
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 fino al tempo che avvenne quello che avea detto, e la parola dell’Eterno, nella prova, gli rese giustizia.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Il re mandò a farlo sciogliere, il dominatore di popoli lo mise in libertà;
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 lo costituì signore della sua casa e governatore di tutti i suoi beni
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 per incatenare i principi a suo talento, e insegnare ai suoi anziani la sapienza.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Allora Israele venne in Egitto, e Giacobbe soggiornò nel paese di Cham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Iddio fece moltiplicar grandemente il suo popolo, e lo rese più potente dei suoi avversari.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Poi voltò il cuor loro perché odiassero il suo popolo, e macchinassero frodi contro i suoi servitori.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Egli mandò Mosè, suo servitore, e Aaronne, che aveva eletto.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Essi compiron fra loro i miracoli da lui ordinati, fecero dei prodigi nella terra di Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Mandò le tenebre e fece oscurar l’aria, eppure non osservarono le sue parole.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Cangiò le acque loro in sangue, e fece morire i loro pesci.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 La loro terra brulicò di rane, fin nelle camere dei loro re.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Egli parlò, e vennero mosche velenose e zanzare in tutto il loro territorio.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Dette loro grandine invece di pioggia, fiamme di fuoco sul loro paese.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Percosse le loro vigne e i loro fichi e fracassò gli alberi del loro territorio.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Egli parlò e vennero le locuste e i bruchi senza numero,
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 che divorarono tutta l’erba nel loro paese e mangiarono il frutto della loro terra.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Poi percosse tutti i primogeniti nel loro paese, le primizie d’ogni loro forza.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 E fece uscire gli Israeliti con argento ed oro, e non vi fu alcuno, fra le sue tribù, che fosse fiacco.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 L’Egitto si rallegrò della loro partenza, poiché la paura d’essi era caduta su loro.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Egli distese una nuvola per ripararli, e accese un fuoco per rischiararli di notte.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 A loro richiesta fece venire delle quaglie, e li saziò col pane del cielo.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Egli aprì la roccia e ne scaturirono acque; esse corsero per luoghi aridi, come un fiume.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Poiché egli si ricordò della sua parola santa e d’Abrahamo, suo servitore;
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 e trasse fuori il suo popolo con allegrezza, e i suoi eletti con giubilo.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 E dette loro i paesi delle nazioni, ed essi presero possesso della fatica dei popoli,
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 perché osservassero i suoi statuti e ubbidissero alle sue leggi. Alleluia.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Salmi 105 >