< Salmi 78 >

1 Maschil di Asaf ASCOLTA, o popol mio, la mia dottrina; Porgete gli orecchi alle parole della mia bocca.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Io aprirò la mia bocca in sentenza; Io sgorgherò detti notevoli [di cose] antiche;
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Le quali noi abbiamo udite, e sappiamo, E le quali i nostri padri ci han raccontate.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Noi non [le] celeremo a' lor figliuoli, alla generazione a venire; Noi racconteremo le lodi del Signore, E la sua forza, e le sue maraviglie ch'egli ha fatte.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Egli ha fermata la testimonianza in Giacobbe, Ed ha posta la Legge in Israele; Le quali egli comandò a' nostri padri di fare assapere a' lor figliuoli;
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 Acciocchè la generazione a venire, i figliuoli [che] nascerebbero, [le] sapessero, [E] si mettessero a narrar[le] a' lor figliuoli;
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 E ponessero in Dio la loro speranza, E non dimenticassero le opere di Dio. Ed osservassero i suoi comandamenti;
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 E non fossero come i lor padri, Generazione ritrosa e ribella; Generazione che non dirizzò il cuor suo, Il cui spirito non [fu] leale inverso Dio.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 I figliuoli di Efraim, gente di guerra, [buoni] arcieri, Voltarono le spalle al dì della battaglia.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Non avevano osservato il patto di Dio, Ed avevano ricusato di camminar nella sua Legge;
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Ed avevano dimenticate le sue opere, E le maraviglie ch'egli aveva lor fatte vedere.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Egli aveva fatti miracoli in presenza de' padri loro, Nel paese di Egitto, nel territorio di Soan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Egli aveva fesso il mare, e li aveva fatti passare per mezzo; Ed aveva fermate le acque come un mucchio.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 E li aveva condotti di giorno colla nuvola, E tutta notte colla luce del fuoco.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Egli aveva schiantate le rupi nel deserto, E li aveva copiosamente abbeverati, come di gorghi;
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Ed aveva fatto uscir de' ruscelli della roccia, E colare acque, a guisa di fiumi.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Ma essi continuarono a peccar contro a lui, Provocando l'Altissimo a sdegno nel deserto;
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 E tentarono Iddio nel cuor loro, Chiedendo vivanda a lor voglia;
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 E parlarono contro a Dio, [E] dissero: Potrebbe Iddio Metterci tavola nel deserto?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Ecco, egli percosse la roccia, e ne colarono acque, E ne traboccarono torrenti; Potrebbe egli eziandio dar del pane, [O] apparecchiar della carne al suo popolo?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Perciò, il Signore, avendoli uditi, si adirò fieramente; Ed un fuoco si accese contro a Giacobbe, Ed anche l'ira [gli] montò contro ad Israele;
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Perciocchè non avevano creduto in Dio, E non si erano confidati nella sua salvazione;
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 E pure egli aveva comandato alle nuvole di sopra, Ed aveva aperte le porte del cielo;
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Ed aveva fatta piovere sopra loro la manna da mangiare, Ed aveva loro dato del frumento del cielo.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 L'uomo mangiò del pane degli Angeli; Egli mandò loro della vivanda a sazietà.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Egli fece levar nel cielo il vento orientale, E per la sua forza addusse l'Austro;
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 E fece piover sopra loro della carne, a guisa di polvere; Ed uccelli, a giusa della rena del mare.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 E [li] fece cadere in mezzo al lor campo, D'intorno a' lor padiglioni.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Ed essi mangiarono, e furono grandemente satollati; E [Iddio] fece lor venire ciò che desideravano.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Essi non si erano [ancora] stolti dalla lor cupidigia; [Avevano] ancora il cibo loro nella bocca,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Quando l'ira montò a Dio contro a loro, Ed uccise i più grassi di loro, Ed abbattè la scelta d'Israele.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Con tutto ciò peccarono ancora, E non credettero alle sue maraviglie.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Laonde egli consumò i lor giorni in vanità, E gli anni loro in ispaventi.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Quando egli li uccideva, essi lo richiedevano, E ricercavano di nuovo Iddio.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 E si ricordavano che Iddio [era] la lor Rocca, E [che] l'Iddio altissimo [era] il lor Redentore.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Ma lo lusingavano colla lor bocca, E gli mentivano colla lor lingua;
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 E il cuor loro non [era] diritto inverso lui, E non erano leali nel suo patto.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 E pure egli, [che è] pietoso, purgò la loro iniquità, e non li distrusse; E più e più volte racquetò l'ira sua, e non commosse tutto il suo cruccio;
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 E si ricordò ch'erano carne; Un fiato che passa, e non ritorna.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Quante volte lo provocarono essi a sdegno nel deserto, [E] lo contristarono nella solitudine!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 E tornarono a tentare Iddio, E limitarono il Santo d'Israele.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Essi non si erano ricordati della sua mano, [Nè] del giorno nel quale li aveva riscossi dal nemico.
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 (Come egli aveva eseguiti i suoi segni in Egitto, E i suoi miracoli nel territorio di Soan.
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Ed aveva cangiati i fiumi, e i rivi degli Egizi in sangue, [Talchè] essi non [ne] potevano bere.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 [Ed] aveva mandata contro a loro una mischia [d'insetti] che li mangiarono; E rane, che li distrussero.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Ed aveva dati i lor frutti a' bruchi, E le lor fatiche alle locuste.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Ed aveva guastate le lor vigne colla gragnuola, E i lor sicomori colla tempesta.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Ed aveva dati alla grandine i lor bestiami, E le lor gregge a' folgori.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 [Ed] aveva mandato sopra loro l'ardore della sua ira, Indegnazione, cruccio e distretta; Una mandata d'angeli maligni.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 [Ed] aveva appianato il sentiero alla sua ira, [E] non aveva scampata l'anima loro dalla morte, Ed aveva dato il lor bestiame alla mortalità.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Ed aveva percossi tutti i primogeniti in Egitto, E le primizie della forza ne' tabernacoli di Cam.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 E [ne] aveva fatto partire il suo popolo, a guisa di pecore; E l'aveva condotto per lo deserto, come una mandra.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 E l'aveva guidato sicuramente, senza spavento; E il mare aveva coperti i lor nemici.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Ed egli li aveva introdotti nella contrada della sua santità, Nel monte [che] la sua destra ha conquistato.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Ed aveva scacciate le nazioni d'innanzi a loro, E le aveva fatte [loro] scadere in sorte di eredità, Ed aveva stanziate le tribù d'Israele nelle loro stanze.)
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Ed avevano tentato, e provocato a sdegno l'Iddio altissimo, E non avevano osservate le sue testimonianze.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Anzi si erano tratti indietro, E si erano portati dislealmente, Come i lor padri; [E] si erano rivolti come un arco fallace;
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 E l'avevano provocato ad ira co' loro alti luoghi, E commosso a gelosia colle loro sculture.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Iddio aveva udite [queste cose], e se n'era gravemente adirato, Ed aveva grandemente disdegnato Israele.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Ed aveva abbandonato il tabernacolo di Silo; Il padiglione ch'egli aveva piantato per sua stanza fra gli uomini.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Ed aveva abbandonata la sua forza, [ad esser menata] in cattività, E la sua gloria in man del nemico.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Ed aveva dato il suo popolo alla spada, E si era gravemente adirato contro alla sua eredità.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Il fuoco aveva consumati i suoi giovani; E le sue vergini non erano state lodate.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 I suoi sacerdoti erano caduti per la spada; E le sue vedove non avevano pianto.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Poi il Signore si risvegliò, Come uno che fosse stato addormentato; Come un [uomo] prode, che dà gridi dopo il vino.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 E percosse i suoi nemici da tergo, E mise loro addosso un eterno vituperio.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Ed avendo riprovato il tabernacolo di Giuseppe, E non avendo eletta la tribù di Efraim;
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Egli elesse la tribù di Giuda; Il monte di Sion, il quale egli ama.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Ed edificò il suo santuario, a guisa di [palazzi] eccelsi; Come la terra [ch]'egli ha fondata in perpetuo.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Ed elesse Davide, suo servitore, E lo prese dalle mandre delle pecore.
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 Di dietro alle [bestie] allattanti Egli lo condusse a pascer Giacobbe, suo popolo; Ed Israele sua eredità.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Ed egli li pasturò, secondo l'integrità del suo cuore; E li guidò, secondo il gran senno delle sue mani.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Salmi 78 >