< Salmi 60 >

1 Mictam di Davide, da insegnare; [dato] al Capo de' Musici, sopra Susan-edut; intorno a ciò ch'egli diede il guasto alla Siria di Mesopotamia, ed alla Siria di Soba; e che Ioab, ritornando, sconfisse gl'Idumei nella valle del Sale, [in numero di] dodici mila O DIO, tu ci hai scacciati, tu ci hai dissipati, Tu ti sei adirato; [e poi], tu ti sei rivolto a noi.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Tu hai scrollata la terra, e l'hai schiantata; Ristora le sue rotture; perciocchè è smossa.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Tu hai fatte sentire al tuo popolo cose dure; Tu ci hai dato a bere del vino di stordimento.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 [Ma ora], tu hai dato a quelli che ti temono una bandiera, Per alzarla, per amor della [tua] verità. (Sela)
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 Acciocchè la tua diletta gente sia liberata, Salva[mi col]la tua destra, e rispondimi.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 Iddio ha parlato per la sua santità: Io trionferò, Io spartirò Sichem, e misurerò la valle di Succot.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Mio [è] Galaad, e mio [è] Manasse, Ed Efraim [è] la forza del mio capo; Giuda [è] il mio legislatore;
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab [è] la caldaia del mio lavatoio; Io getterò le mie scarpe sopra Edom; O Palestina, fammi delle acclamazioni.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Chi mi condurrà nella città della fortezza? Chi mi menerà fino in Edom?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Non [sarai desso] tu, o Dio, [che] ci avevi scacciati? E non uscivi [più] fuori, o Dio, co' nostri eserciti?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Dacci aiuto, [per uscir] di distretta; Perciocchè il soccorso degli uomini [è] vanità.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 In Dio noi faremo prodezze; Ed egli calpesterà i nostri nemici.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< Salmi 60 >