< Salmi 15 >

1 Salmo di Davide O SIGNORE, chi dimorerà nel tuo tabernacolo? Chi abiterà nel monte della tua santità?
Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
2 Colui che cammina in integrità, e fa ciò che è giusto, E parla il vero di cuore;
Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
3 Che non dice male colla sua lingua, [E] non fa male alcuno al suo compagno, E non leva alcun vituperio contro al suo prossimo;
ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
4 Appo cui è sprezzato chi deve esser riprovato, E che onora quelli che temono il Signore; [E il quale, se] ha giurato alcuna cosa, [Benchè sia] a [suo] danno, non però la ritratta;
wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
5 [Il quale] non dà i suoi danari ad usura. E non prende presenti contro all'innocente. Chi fa queste cose non sarà giammai smosso.
wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.

< Salmi 15 >