< Salmi 135 >

1 ALLELUIA. Lodate il Nome del Signore; Lodate[lo, voi] servitori del Signore;
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Che state nella Casa del Signore, Ne' cortili della Casa del nostro Dio.
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Lodate il Signore; perciocchè il Signore [è] buono; Salmeggiate al suo Nome, perciocchè [è] amabile.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Conciossiachè il Signore si abbia eletto Giacobbe [Ed] Israele per suo tesoro riposto.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Certo io conosco che il Signore [è] grande, E che il nostro Signore [è maggiore] di tutti gl'iddii.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Il Signore fa tutto ciò che gli piace In cielo ed in terra; Ne' mari, ed [in] tutti gli abissi.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Egli fa salire i vapori dall'estremità dalle terra; Egli fa i lampi per la pioggia; Egli trae fuori il vento da' suoi tesori.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 [Egli è quel] che percosse i primogeniti di Egitto, Così degli uomini, come degli animali.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 Che mandò segni e prodigi, in mezzo di te, o Egitto; Sopra Faraone, e sopra tutti i suoi servitori.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Che percosse nazioni grandi, Ed uccise re potenti;
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon, re degli Amorrei, E Og, re di Basan, E i re di tutti i regni di Canaan;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 E diede i lor paesi per eredità, Per eredità ad Israele, suo popolo.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 O Signore, il tuo Nome [è] in eterno; O Signore, la memoria di te [è] per ogni età.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Quando il Signore avrà fatti i suoi giudicii sopra il suo popolo, Egli si pentirà per amor de' suoi servitori.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Gl'idoli delle genti[sono] argento ed oro, Opera di mani d'uomini;
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Hanno bocca, e non parlano; Hanno occhi, e non veggono;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Hanno orecchi, e non odono; [Ed] anche non hanno fiato alcuno nella lor bocca.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Simili ad essi sieno quelli che li fanno; Chiunque in essi si confida.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Casa d'Israele, benedite il Signore; Casa d'Aaronne, benedite il Signore.
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Casa di Levi, benedite il Signore; [Voi] che temete il Signore, beneditelo.
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Benedetto [sia] da Sion il Signore, Che abita in Gerusalemme. Alleluia.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Salmi 135 >