< Salmi 107 >

1 CELEBRATE il Signore; perciocchè [egli è] buono. Perciocchè la sua benignità [dura] in eterno.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 [Così] dicano quelli che sono stati riscattati dal Signore, I quali egli ha riscossi di distretta.
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 E li ha raccolti da' [diversi] paesi, Dal Levante e dal Ponente; dal Settentrione e dal mare.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Essi andavano errando per deserti, per cammini di solitudine; Non trovavano città abitata.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 [Erano] affamati ed assetati; L'anima loro spasimava in loro.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Ma, avendo gridato al Signore, mentre erano in distretta, Egli li ha tratti fuor delle loro angosce;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 E li ha condotti per diritto cammino, Per andare in città abitata.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Celebrino [adunque] appo il Signore la sua benignità, E le sue maraviglie appo i figliuoli degli uomini.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Perciocchè egli ha saziata l'anima assetata, Ed ha empiuta di beni l'anima affamata.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 [Così dicano] quelli che dimoravano in tenebre ed in ombra di morte, Prigioni, [ritenuti] in afflizione, e ne' ferri.
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Perciocchè erano stati ribelli alle parole del Signore, Ed avevano sprezzato il consiglio dell'Altissimo;
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Onde egli aveva abbattuto il cuor loro con affanni, [Ed] erano caduti; e non [vi era] alcuno che [li] soccorresse.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Ma, avendo gridato al Signore, mentre erano in distretta, Egli li ha salvati dalle loro angosce;
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 [E] li ha tratti fuor delle tenebre, e dell'ombra della morte; Ed ha rotti i lor legami.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Celebrino [adunque] appo il Signore la sua benignità, E le sue maraviglie appo i figliuoli degli uomini.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Perciocchè egli ha rotte le porte di rame, Ed ha spezzate le sbarre di ferro.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 [Così dicano] gli stolti, [ch]'erano afflitti per li lor misfatti, Ne' quali camminavano, e per le loro iniquità.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 La cui anima abbominava ogni cibo; Ed erano giunti fino alle porte della morte.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Ma, avendo gridato al Signore, mentre erano in distretta, Egli li ha salvati dalle loro angosce.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Egli ha mandata la sua parola, e li ha sanati, E liberati dalle lor malattie mortali.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Celebrino [adunque] appo il Signore la sua benignità, E le sue maraviglie appo i figliuoli degli uomini.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 E sacrifichino sacrificii di lode, E raccontino le sue opere con giubilo.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 [Così dicano] quelli che scendono nel mare sopra navi, Che fanno traffico su per le grandi acque.
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Essi veggono le opere del Signore, E le sue maraviglie nel profondo [mare].
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Perciocchè, alla sua parola, egli fa levare il vento di tempesta, Il quale alza le onde di esso.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Salgono al cielo, [poi] scendono agli abissi; L'anima loro si strugge di male.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Saltano, e traballano come un ebbro; E perdono tutto il lor senno.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Ma, gridando al Signore, mentre sono in distretta, Egli li trae fuor delle loro angosce.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Egli acqueta la tempesta, E le onde loro si fermano.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Ed essi si rallegrano che sono acquetate; Ed egli li conduce al porto da loro desiderato.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Celebrino [adunque] appo il Signore la sua benignità, E le sue maraviglie appo i figliuoli degli uomini.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Ed esaltinlo nella raunanza del popolo, E laudinlo nel concistoro degli anziani.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Egli riduce i fiumi in deserto, E le vene delle acque in luoghi aridi;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 La terra fertile in salsuggine, Per la malvagità de' suoi abitanti.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Egli riduce i deserti in guazzi d'acque. E la terra arida in vene d'acque;
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 E fa quivi abitar gli affamati, I quali [vi] fondano città da abitare.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 E seminano campi, e piantano vigne, Che producono rendita di frutto.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Ed egli li benedice, e moltiplicano grandemente; Ed egli non iscema i lor bestiami.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Poi vengono al meno, e sono abbassati Per distretta, [per] avversità, e [per] affanni.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Egli spande lo sprezzo sopra i nobili, E li fa andare errando per luoghi deserti, [ove] non [vi è] via alcuna.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 E innalza il bisognoso dalla miseria, E fa che le famiglie [moltiplicano] a guisa di gregge.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Gli [uomini] diritti, veggendo [queste cose], si rallegrano; Ma ogni iniquità si tura la bocca.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Chi [è] savio? osservi queste cose, E consideri le benignità del Signore.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Salmi 107 >