< Giosué 21 >

1 OR i Capi delle [nazioni] paterne dei Leviti vennero al Sacerdote Eleazaro, e a Giosuè, figliuolo di Nun, e ai Capi delle [nazioni] paterne delle tribù de' figliuoli d'Israele;
To, a lokacin, sai shugabannin iyalan Lawiyawa suka je wurin Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin sauran iyalan kabilu na Isra’ila a
2 e parlarono loro, in Silo, nel paese di Canaan, dicendo: Il Signore comandò per Mosè, che ci fossero date delle città da abitare, insieme co' lor contorni per lo nostro bestiame.
Shilo cikin Kan’ana, suka ce musu, “Ubangiji ya yi umarni ta wurin Musa cewa a ba mu garuruwan da za mu zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau don dabbobinmu.”
3 E i figliuoli d'Israele diedero della loro eredità a' Leviti, secondo il comandamento del Signore, queste città co' lor contorni.
Saboda haka kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo daga cikin gādonsu.
4 E la sorte essendo tratta per le nazioni de' Chehatiti, scaddero a sorte a' figliuoli del Sacerdote Aaronne, d'infra i Leviti, tredici città della tribù di Giuda, e della tribù di Simeone, e della tribù di Beniamino.
Ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kan Kohatawa bisa ga iyalansu. Sai aka ba wa Lawiyawa waɗanda suke’yan zuriyar Haruna, firist, garuruwa goma sha uku daga kabilan Yahuda, Simeyon da Benyamin.
5 E al rimanente de' figliuoli di Chehat, [scaddero] a sorte dieci città delle nazioni della tribù di Efraim, e della tribù di Dan, e della mezza tribù di Manasse.
Sauran Kohatawan kuma aka ba su garuruwa goma daga iyalan kabilar Efraim, Dan da kuma rabi kabilar Manasse.
6 E a' figliuoli di Gherson [scaddero] a sorte tredici città delle nazioni della tribù d'Issacar, e della tribù di Aser, e della tribù di Neftali, e della mezza tribù di Manasse, in Basan.
Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.
7 Ai figliuoli di Merari, secondo le lor nazioni, [scaddero] dodici città, della tribù di Ruben, e della tribù di Gad, e della tribù di Zabulon.
Aka ba wa zuriyar Merari bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga kabilan Ruben, Gad da Zebulun.
8 I figliuoli d'Israele adunque diedero queste città, co' lor contorni, a' Leviti a sorte; come il Signore avea comandato per Mosè.
Haka Isra’ilawa suka ba wa Lawiyawa waɗannan garuruwa da wuraren kiwo masu kyau, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
9 Diedero, dico, della tribù de' figliuoli di Giuda, e della tribù de' figliuoli di Simeone, queste città, che saranno nominate per nome;
Daga kabilan Yahuda da Simeyon ne aka ba su waɗannan garuruwan da aka ambata,
10 le quali i figliuoli di Aaronne, d'infra le nazioni de' Chehatiti, d'infra i figliuoli di Levi, ebbero; perciocchè la prima sorte fu per loro.
(ga garuruwan da aka ba wa zuriyar Haruna waɗanda suke daga iyalan Kohatawa na Lawiyawa, domin ƙuri’a ta farko ta fāɗa a kansu),
11 Diedero adunque loro la città di Arba, padre di Anac, [che] è Hebron, nel monte di Giuda, co' suoi contorni.
an ba su, Kiriyat Arba (wato, Hebron), da wurin kiwon da yake kewaye da ƙasar kan tudu ta Yahuda. (Arba shi ne kakan Anak.)
12 Ma diedero il territorio della città, e le sue villate, a Caleb, figliuolo di Gefunne, per sua possessione.
Amma sai aka ba Kaleb ɗan Yefunne filayen da kuma ƙauyukan da suke kewaye da birnin, su zama nasa.
13 Così diedero a' figliuoli del Sacerdote Aaronne la città del rifugio dell'ucciditore, [cioè] Hebron e i suoi contorni; e Lebna, e i suoi contorni;
Sai aka ba zuriyar Haruna firist, ƙasar Hebron (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Libna,
14 e Iattir e i suoi contorni; ed Estemoa e i suoi contorni;
da Yattir, da Eshtemowa,
15 e Holon e i suoi contorni; e Debir e i suoi contorni;
da Holon, da Debir,
16 e Ain e i suoi contorni; e Iutta e i suoi contorni; e Bet-semes e i suoi contorni; nove città di queste due tribù.
da Ayin, da Yutta, da kuma Bet-Shemesh, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa tara ke nan daga kabilun nan biyu, Yahuda da Simeyon.
17 E della tribù di Beniamino, Ghibon e i suoi contorni; Gheba e i suoi contorni;
Daga kabilar Benyamin kuwa aka ba su, Gibeyon, Geba,
18 Anatot e i suoi contorni; e Almon e i suoi contorni; quattro città.
Anatot da Almon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
19 Tutte le città de' figliuoli di Aaronne, sacerdoti, [furono] tredici città co' lor contorni.
Duka-duka garuruwan firistoci, zuriyar Haruna, su goma sha uku ne tare da wuraren kiwonsu.
20 Poi le nazioni de' figliuoli di Chehat, Leviti, [cioè], il rimanente de' figliuoli di Chehat, ebbero le città della lor sorte della tribù di Efraim.
Aka kuma ba wa sauran Kohatawa, iyalan Lawiyawa, garuruwa daga kabilar Efraim.
21 E furono loro date, la città del rifugio dell'ucciditore, [cioè: ] Sichem e i suoi contorni, nel monte di Efraim; e Ghezer e i suoi contorni; e Chibsaim e i suoi contorni;
A ƙasar kan tudu ta Efraim, aka ba su, Shekem (garin masu neman mafaka don sun yi kisa) da Gezer,
22 e Bet-horon e i suoi contorni; quattro città;
Kibzayim da Bet-Horon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
23 e della tribù di Dan, Elteche e i suoi contorni; Ghibbeton e i suoi contorni;
Haka kuma daga kabilar Dan, aka ba su, Elteke, Gibbeton,
24 Aialon, e i suoi contorni; Gat-rimmon e i suoi contorni; quattro città.
Aiyalon da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
25 E della mezza tribù di Manasse, Taanac e i suoi contorni; e Gat-rimmon e i suoi contorni; due città.
Daga rabin kabilar Manasse kuwa aka ba su, Ta’anak da Gat-Rimmon, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan.
26 Tutte le città del rimanente delle nazioni de' figliuoli di Chehat [furono] dieci, co' lor contorni.
Dukan garuruwan nan goma tare da wuraren kiwonsu ne aka ba sauran iyalan Kohatawa.
27 Poi a' figliuoli di Gherson, [ch'erano] delle nazioni de' Leviti, [furono date] della mezza tribù di Manasse, la città del rifugio dell'ucciditore, [cioè: ] Golan in Basan e i suoi contorni; e Beestera e i suoi contorni; due città.
Aka ba wa zuriyar Gershon, waɗanda suke Lawiyawa, rabo. Daga rabin kabilar Manasse, Golan a cikin Bashan (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), da Be’eshtera, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa biyu ke nan;
28 E della tribù d'Issacar, Chision e i suoi contorni; Dabrat e i suoi contorni;
daga kabilar Issakar kuma aka ba su Kishiyon, Daberat,
29 Iarmut e i suoi contorni; ed En-gannim e i suoi contorni; quattro città.
Yarmut da En Gannim, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
30 E della tribù di Aser, Miseal e i suoi contorni; Abdon e i suoi contorni;
daga kabilar Asher kuwa aka ba su, Mishal, Abdon,
31 Helcat e i suoi contorni; e Rehob e i suoi contorni; quattro città.
Helkat da Rehob, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
32 E della tribù di Neftali, la città del rifugio dell'ucciditore, [cioè: ] Chedes in Galilea e i suoi contorni; Hammot-dor e i suoi contorni; e Cartan e i suoi contorni; tre città.
daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.
33 Tutte le città dei Ghersoniti, secondo le lor nazioni, [furono] tredici, co' lor contorni.
Duka-duka, garuruwan iyalan Gershonawa goma sha uku ne, tare da wuraren kiwonsu.
34 Poi alle nazioni de' figliuoli di Merari, [ch'erano] il rimanente de' Leviti, [furono date] della tribù di Zabulon, Iocneam e i suoi contorni; Carta e i suoi contorni;
Aka ba wa iyalan Merari (sauran Lawiyawa) garuruwa, daga kabilar Zebulun, wato, Yokneyam, Karta,
35 Dimna e i suoi contorni; Nahalal e i suoi contorni; quattro città.
Dimna da kuma Nahalal, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
36 E della tribù di Ruben, Beser e i suoi contorni; e Iasa e i suoi contorni;
daga kabilar Ruben kuma aka ba su, Bezer, Yahza,
37 Chedemot e i suoi contorni; e Mefaat e i suoi contorni; quattro città.
Kedemot da kuma Mefa’at, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan;
38 E della tribù di Gad, la città del rifugio dell'ucciditore, [cioè: ] Ramot in Galaad e i suoi contorni; e Mahanaim e i suoi contorni;
daga kabilar Gad kuwa aka ba su, Ramot Gileyad (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Mahanayim,
39 Hesbon e i suoi contorni; Iazer e i suoi contorni; in tutto quattro città.
Heshbon da kuma Yazer, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa huɗu ke nan.
40 Tutte quelle città [furono date] a' figliuoli di Merari, secondo le lor nazioni, [ch'erano] il rimanente delle nazioni, de' Leviti; e la lor sorte fu di dodici città.
Duka-duka garuruwan da aka ba iyalan mutanen Merari, waɗanda su ne sauran Lawiyawa, garuruwa goma sha biyu ne.
41 Tutte le città de' Leviti, per mezzo la possessione de' figliuoli d'Israele, [furono] quarantotto, co' lor contorni.
Jimillar birane da wurarensu na kiwon da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama’ar Isra’ila guda arba’in da takwas ne.
42 Ciascuna di queste città avea i suoi contorni; e così [fu osservato] in tutte quelle città.
Dukan garuruwan nan kowannensu yana kewaye da wurin kiwo.
43 Il Signore adunque diede ad Israele tutto il paese ch'egli aveva giurato ai padri loro di dar loro; e i [figliuoli d'Israele] ne presero la possessione, e abitarono in esso.
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa dukan ƙasar da ya yi wa kakanninsu alkawari, suka kuwa mallake ta, suka zauna a cikinta.
44 E il Signore diede loro riposo d'ogn'intorno, interamente come avea giurato a' lor padri; e niuno, d'infra tutti i lor nemici, potè stare a fronte a loro: il Signore diede loro nelle mani tutti i lor nemici.
Ubangiji ya ba su hutawa a kowane gefe kamar yadda ya yi wa kakanninsu alkawari, ba ko ɗaya daga cikin abokan gābansu da ya iya cinsu da yaƙi.
45 Ei non cadde a terra pure una parola di tutto il bene che il Signore avea detto alla casa d'Israele; ogni cosa avvenne.
Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alherin da ya yi wa mutanen Isra’ila.

< Giosué 21 >