< Isaia 54 >

1 GIUBILA, o sterile, [che] non partorivi; fa' risonar grida di allegrezza, e strilla, [o tu, che] non avevi dolori di parto; perciocchè i figliuoli della desolata [saranno] in maggior numero che quelli della maritata, ha detto il Signore.
“Ki rera, ya ke bakararriya, ke da ba ki taɓa haihuwa ba; ki ɓarke da waƙa, ki yi sowa don farin ciki, ke da ba ki taɓa naƙuda ba; domin’ya’yan mace mai kaɗaici sun fi na mai miji yawa,” in ji Ubangiji.
2 Allarga il luogo del tuo padiglione, e sieno tesi i teli de' tuoi tabernacoli; non divietar[lo: ] allunga le tue corde, e ferma i tuoi piuoli.
“Ki fadada wurin tentinki, ki miƙe labulen tentinki da fāɗi, kada ki janye; ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta.
3 Perciocchè tu moltiplicherai, traboccando a destra ed a sinistra; e la tua progenie possederà le genti, e renderà abitate le città deserte.
Gama za ki fadada zuwa dama da hagu; zuriyarki za su kori al’ummai su kuma zauna a kufan biranensu.
4 Non temere, perciocchè, tu non sarai confusa; e non vergognarti, perciocchè tu non sarai adontata; anzi dimenticherai la vergogna della tua fanciullezza, e non ti ricorderai [più] del vituperio della tua vedovità.
“Kada ki ji tsoro; ba za ki sha kunya ba. Kada ki ji tsoron wulaƙanci, ba za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da kunyar ƙuruciyarki ba kuwa za ki tuna da zargin zaman gwauruwarki ba.
5 Perciocchè il tuo marito [è] quel che ti ha fatta; il suo Nome [è: ] Il Signor degli eserciti; e il tuo Redentore [è] il Santo d'Israele, il [quale] sarà chiamato l'Iddio di tutta la terra.
Gama Mahaliccinki shi ne mijinki, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ne Mai Fansarki; ana ce da shi Allahn dukan duniya.
6 Perciocchè il Signore ti ha chiamata, come una donna abbandonata, e tribolata di spirito; e [come] una moglie sposata in giovanezza, che sia stata mandata via, ha detto il tuo Dio.
Ubangiji zai kira sai ka ce ke mace ce da aka yashe ta tana kuma damuwa a ranta, macen da ta yi aure a ƙuruciya, sai kawai aka ƙi ta,” in ji Allahnki.
7 Io ti ho lasciata per un piccol momento, ma ti raccoglierò per grandi misericordie.
“Gama a ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, amma da ƙauna mai zurfi zan sāke dawo da ke.
8 Io ho nascosta la mia faccia da te per un momento, nello stante dell'indegnazione; ma ho avuta pietà di te per benignità eterna, ha detto il Signore, tuo Redentore.
Cikin fushi mai zafi na ɓoye fuskata daga gare ki na ɗan lokaci, amma da madawwamin alheri zan ji tausayinki,” in ji Ubangiji Mai Fansarki.
9 Perciocchè questo mi [sarà come] le acque di Noè; conciossiachè, [come] io giurai che le acque di Noè non passerebbero più sopra la terra, così ho giurato che non mi adirerò [più] contro a te, e non ti sgriderò [più].
“A gare ni wannan ya yi kamar kwanakin Nuhu, sa’ad da na rantse cewa ruwan Nuhu ba za su ƙara rufe duniya ba. Yanzu fa na rantse ba zan yi fushi da ke ba, ba zan ƙara tsawata miki kuma ba.
10 Avvegnachè i monti si dipartissero [dal luogo loro], e i colli si smovessero; pur non si dipartirà la mia benignità da te, e il patto della mia pace non sarà smosso; ha detto il Signore, che ha pietà di te.
Ko da duwatsu za su girgiza a kuma tumɓuke tuddai, duk da haka madawwamiyar ƙaunata da nake yi miki ba za tă jijjigu ba ba kuwa za a kawar da alkawarin salamata ba,” in ji Ubangiji, wanda ya ji tausayinki.
11 O afflitta, tempestata, sconsolata; ecco, io poserò le tue pietre sopra marmo fino, e ti fonderò sopra zaffiri.
“Ya ke birni mai shan azaba, wadda hadari ya bulale ki ba a kuma ta’azantar da ke ba, zan gina ke da duwatsu turkuwoyis, zan kafa harsashenki da duwatsun saffaya.
12 E farò le tue finestre di rubini e le tue porte di pietre di carbonchi, e tutto il tuo recinto di pietre preziose.
Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske, dukan katangarki kuma da duwatsu masu daraja.
13 E tutti i tuoi figliuoli [saranno] insegnati dal Signore; e la pace de' tuoi figliuoli [sarà] grande.
Ubangiji zai koya wa dukan’ya’yanki maza, da girma kuma salamar’ya’yanki zai zama.
14 Tu sarai stabilita in giustizia, tu sarai lontana d'oppressione, sì che non [la] temerai; e di ruina, sì ch'ella non si accosterà a te.
Da adalci za a kafa ke. Zalunci zai yi nesa da ke; ba za ki kasance da wani abin da za ki ji tsoro ba. Za a kawar da duk wani abin banrazana; ba zai yi kusa da ke ba.
15 Ecco, ben si faranno delle raunate, [ma] non da parte mia; chi si radunerà contro a te, [venendo]ti addosso, caderà.
In wani ya far miki, ba daga wurina ba ne; duk wanda ya far miki zai miƙa wuya gare ki.
16 Ecco, io ho creato il fabbro che soffia il carbone nel fuoco, e che trae fuori lo strumento, per fare il suo lavoro; ed io ancora ho creato il guastatore, per distruggere.
“Duba, ni ne wanda na halicci maƙeri wanda yake zuga garwashi ya zama harshen wuta ya kuma ƙera makamin da ya dace da aikinsa. Ni ne kuma na halicci mai hallakarwa ya yi ɓarna;
17 Niun'arme fabbricata contro a te prospererà; e tu condannerai ogni lingua [che] si leverà contro a te in giudicio. Quest'[è] l'eredità de' servitori del Signore, e la lor giustizia da parte mia, dice il Signore.
ba makamin da aka ƙera don yă cuce ki da zai yi nasara, za ki kuma mayar da magana ga duk wanda ya zarge ki. Wannan ne gādon bayin Ubangiji, kuma wannan ita ce nasararsu daga gare ni,” in ji Ubangiji.

< Isaia 54 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark