< 2 Corinzi 6 >

1 OR essendo operai nell'opera [sua, vi] esortiamo ancora che non abbiate ricevuta la grazia di Dio in vano
A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
2 (perciocchè egli dice: Io ti ho esaudito nel tempo accettevole, e ti ho aiutato nel giorno della salute. Ecco ora il tempo accettevole, ecco ora il giorno della salute);
Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
3 non dando intoppo alcuno in cosa veruna, acciocchè il ministerio non sia vituperato.
Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
4 Anzi, rendendoci noi stessi approvati in ogni cosa, come ministri di Dio, in molta sofferenza, in afflizioni, in necessità, in distrette,
A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
5 in battiture, in prigioni, in turbamenti, in travagli, in vigilie, in digiuni;
Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
6 in purità, in conoscenza, in pazienza, in benignità, in Ispirito Santo, in carità non finta;
Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
7 in parola di verità, in virtù di Dio, con le armi di giustizia a destra ed a sinistra;
da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
8 per gloria, e per ignominia; per buona fama, e per infamia;
ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
9 come seduttori, e [pur] veraci; come sconosciuti, e [pur] riconosciuti; come morenti, e [pure] ecco viviamo; come castigati, ma [pure] non messi a morte;
mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
10 come contristati, e [pur] sempre allegri; come poveri, e [pure] arricchendo molti; come non avendo nulla, e [pur] possedendo ogni cosa.
cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
11 LA nostra bocca è aperta inverso voi, o Corinti; il cuor nostro è allargato.
Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
12 Voi non siete allo stretto in noi, ma ben siete stretti nelle vostre viscere.
Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
13 Ora, per [far] par pari, io parlo come a figliuoli, allargatevi ancora voi.
A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
14 Non vi accoppiate con gl'infedeli; perciocchè, che partecipazione [vi è] egli tra la giustizia e l'iniquità? e che comunione [vi è] egli della luce con le tenebre?
Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
15 E che armonia [vi è] egli di Cristo con Belial? o che parte ha il fedele con l'infedele?
Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
16 E che accordo [vi è] egli del tempio di Dio con gl'idoli? poichè voi siete il tempio dell'Iddio vivente; siccome Iddio disse: Io abiterò nel mezzo di loro, e camminerò fra [loro]; e sarò lor Dio, ed essi mi saranno popolo.
Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
17 Perciò, dipartitevi del mezzo di loro, e separatevene, dice il Signore; e non toccate nulla d'immondo, ed io vi accoglierò;
Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
18 e vi sarò per padre, e voi mi sarete per figliuoli e per figliuole, dice il Signore Onnipotente.
Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< 2 Corinzi 6 >